Connect with us

Kungiyoyi

Kwanaki 100: Jagorancin Asma’u A Matsayin Shugabar NUJ Kaduna Ta Yi Tasiri

Published

on

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

KAMAR ba a taba yin irinsa ba, Kungiyar yan Jaridu ta Najeriya (NUJ) reshen Jihar Kaduna ta samu gagarumin ci gaba, musamman a fannin samar da yanayi mai kyau ga mambobinta wanda a halin yanzu ke taimaka wa kwararru da kwazon da ake bukata daga kwararrun ‘yan Jaridu, kuma babu shakka yanayin kwanciyar hankali ya haifar da wani matakin mutunta kungiyar.

Asma’u Yawo Halilu, ta kasance a cikin tarihi, kasancewarta mace ta farko da ta fara shugabantar kungiyar NUJ Kaduna, kuma ta biyu a fadin kasar nan. A matsayin mace mai tarihi; Asma’u tana yunƙurin rubuta sunanta da zinare a matsayin mai hazaka, tare da irin nasarorin da aka samu a bayyane a cikin kwanaki 100 na aikinta, wanda ko shakka babu Asma’u ta kasance zakaran gwajin dafi.

Ƙarfinta, ƙwazo a ofis, ikhlasi na zuciya da manufa, balaga wajen tafiyar da al’amura, da kasancewarta mai kwazo musamman wajen tunkarar batutuwan da suka shafi jin daɗin membobinta sun riga sun tabbatar da furcin nan da ya ce: ‘Abin da namiji zai iya yi, mace za ta iya yin fiye da hakan, idan aka yi la’akari da yanayin hangen nesanta.

Kamar yadda ta ce a lokacin yakin neman zabenta, burinta shi ne tabbatar da cewa dukkan ‘ya’yan kungiyar NUJ ta Kaduna sun samu tasirin shugabancinsu da kuma tabbatar da kwarewa, kuma sun yi alkawarin samar da yanayi mai kyau ga mambobin kuma zasu cika su a hankali domin a bayyane suke.

Acewarta, ” Jin dadin mambobinsu ne hanyar budin su a matsayinmu na shugabanni, hakazalika ba da fifiko ga jin dadin Jama’a ba shakka zai mayar da Kungiyar zuwa lokutan daukaka da girmamawa a tsakanin mambobinta,” in ji Asma’u.

To sai dai kuma duk wanda ke da masaniyar Kungiyar NUJ ta Kaduna kafin zuwa Asmau Yawo Halilu a cikin kwanaki 100 da suka gabata, na iya shaida cewa yanayin shugabancin ta na kan turbar da ta dace domin kuwa a yau duk wanda ya zo Sakatariyar ta NUJ, tambayar farko a bakinsa ita ce wane ne ke Shugabantar cibiyar Kungiyar NUJ ta Kaduna?

A cikin mafi kankanin lokaci, an dawo da kwarin gwiwar membobin wanda hakan ya biyo bayan bayyana gaskiya da rashin rikon sakainar kashi na shugabancinta, wanda acewarta “Gaskiya da rikon amana ne abin lura a shugabancinmu, hadin kan ‘ya’yan Kungiyarmu ma shi ne abin da na sa a gaba, addu’armu ita ce Allah Madaukakin Sarki Ya kiyaye mu Ya kuma yi mana jagora Ya ba mu damar cika alkawuran yakin neman zabe da muka daukarwa al’ummarmu,” in ji Asma’u.

Hankalin Asmau da sanin ya kamata da kasancewarta mai kirki mai ruhin afuwa da kokarin hada kan al’ummarta su ne kyawawan dabi’un da suka ja hankalin ‘yan Kungiyar zuwa gare ta, kuma babu shakka Asma’u ta kasance mai canza wasa, shugaba mai kishin kasa da hangen nesa wanda a halin da ake ciki na shugabancinta, ta samar da ofishi ga kungiyar masu aiko da rahotanni a Sakatariyar kungiyar NUJ Kaduna.

“Dalilin da ya sani wannan tunanin shi ne don inganta haɗin kai a tsakanin mambobinmu. Kuma bayan haka, ba abin jin dadi ba cewa kungiyar na kokawa don biyan kuɗin ofishin haya. Hakazalika a yanzu muna kuma aiki a kan Kungiyar Mata Yan Jaridu wato (NAWOJ), ta yadda ‘yan Jarida mata za su iya samun ofishin nasu a cikin ita Sakatariyar ta NUJ, domin hakki ne a kanmu a matsayinmu na shugabanni mu tabbatar da cewa mambobinmu suna aiki yadda ya kamata,” inji ta.

Ta ci gaba da cewa, harkokin wasanni na Kungiyar da suka yi fama rashin kulawa da aka yi watsi da su na tsawon shekaru za a dawo da su, yayin da aka fara aiki kan yadda ake samun Gidan Wasanni, domin burin Asma’u shi ne a samu gidan Wasanni mai cike da kayan aiki na zamani kuma tuni wannan yunkurin ya fara kankama.

“Wadannan halaye ne da muka gani a Asma’u, kuma muna farin cikin ganin alkawuran da ta yi na yakin neman zabe ana aiwatar da su daya bayan daya, muna da imanin cewa za ta iya yin abin da ya dace da goyon bayan mambobin wanda ayyukanta sun ba mu mamaki. A cikin wannan dan karamin lokaci, ta taka rawar gani sosai,” in ji tsohon shugaban cibiyar Kungiyar Yan Jaridu na Kamfanin NNN, Nicholas Dekera.

Har ila yau, a karon farko a tarihin kungiyar NUJ ta Kaduna, karkashin Jagorancin Asma’u ta gabatar da Thrift and Co-operative Society ga mambobi Kungiyar NUJ. Haka kuma bayyanar sabbin shuwagabannin an sake dawo da kwas na Cibiyar Nazarin Jarida ta Duniya (IIJ) wacce aka dakatar da ita na tsawon shekaru.

A cikin wannan lokacin, Ƙungiyar ta kuma haɗa gwiwa da Kamfanin lemon kwalba ta 7up domin sake yin fentin Sakatariyar wanda cika sharuddan ya sanya sabon salo ga Sakatariyar.

Har ila yau, a kwanakin baya ne dai salon Shugabancin Asma’u ya baiwa kungiyar damar samun wata mota kirar Ford galaxy, wanda Sanata mai wakiltar Kaduna ta tsakiya Malam Uba Sani ya bayar. Hakazalika an gudanar da horon jagoranci ga wasu mambobin kungiyar zartaswa na Jiha (SEC) da gidauniyar ci gaban kafofin watsa labarai ta Afrika (AMDF) ta yi, wanda wannan wani mataki ne na jagorancin Asma’u.

Shugaban kungiyar FRCN, Umar Adamu Sarkin Fada, ya bayyana cewa, ” horon kan Jagoranci ya samu nasara wajen tsara tunanin shugabannin Kungiyar nasu kan yadda za su jagoranci al’ummar su.

Kafin fitowarta, babu wani bandaki guda ɗaya mai aiki, (toilet) a cikin sakatariyar membobin Kungiyar. Sai dai a yau labari ya sauya inda sabbin shugabannin da Asma’u ta ke jagoranta suka inganta bandakin da aka yi watsi da su domin amfanin al’ummar.

A bisa irin nasarorin da aka gani kuma aka rubuta ya zuwa yanzu, ai ko makaho ma na iya ji, wato a takaice yanzu ba labari bane cewa kasancewar Asma’u Yawo Halilu a matsayin shugaba, Daniel Duniya mataimakin shugaba, Gambo Santos a matsayin sakatare, Salisu Ibrahim a matsayin Auditor, Gabriel Idibia a matsayin Ex-officio 1 da Matata Abdullahi a matsayin Ex-officio. 2, tuni suna jagorantar Kungiyar izuwa ga nasara.

A cikin wannan ‘Tafiya ta Canji’, kyakkyawar manufa Asma’u ya riga ya sanya Kungiyar a kan wani matsayi na kishin samun nasara.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Kungiyoyi

Ƙungiyoyin musulunci sun raba wa marayu 900 abinci kyauta a Katsina (Hotuna)

Published

on

Daga Abbas Bamalli

A wani biki mai ƙayatarwa da aka gudanar a gidan marayu na Katsina, sama da marayu 900 ne suka sami farin ciki matuƙa a lokacin da suka samu liyafar cin abincin rana, wanda ƙungiyoyi masu zaman kansu na Musulunci na ƙasa da ƙasa suka yi shirya.

Amir Sultana daga ƙasar Turkiyya tare da haɗin gwiwar Munazzama Da’awa Al-Islam (MADA) daga ƙasar Sudan ne suka shirya taron tare da haɗin gwiwar ofishin uwargidan gwamnan jihar Katsina, Hajiya Zulaihat Raɗɗa.

Shugaban ƙungiyoyi masu zaman kansu, Mufti Ahmed, ya bayyana cewa kimanin marayu 700 a ƙaramar hukumar Katsina da 200 a Jibiya ne suka ci gajiyar wannan kyakkyawan shiri.

Ahmed ya jaddada cewa manufarsu ita ce sanya murmushi a fuskokin marasa galihu, musamman marayu, da ke nuna irin yadda ƙungiyoyin ke gudanar da ayyukan jin ƙai.

KU KUMA KARANTA: Zulum ya raba wa iyalai dubu 40 tallafin abinci da kuɗi a Konduga

An samo kuɗaɗe don shirin ne ta hanyar gudumawa daga mawadata da ɗaiɗaikun mutane da suka amince da ƙungiyoyi masu zaman kansu.

Mufti Ahmed ya bayyana cewa, “Ta hanyar tallafin mun gina rijiyoyin burtsatse kusan 36 a wurare daban-daban a jihar.”

Ya ci gaba da cewa, “Yana daga cikin shirinmu na yin amfani da ragowar kuɗaɗen wajen sanya murmushi a fuskokin marasa galihu, musamman marayu a cikin al’ummarmu.

Wani ɓangare na ayyukanmu shi ne rarraba Alƙur’ani mai girma da kuma bayar da tallafin kuɗi ga marasa galihu.” Baya ga cin abincin rana, ƙungiyoyin sun kuma bayar da gudummawar dalar Amurka 400 ga marayun, wanda hakan ya ƙara haɓaka tasirin ayyukansu na alheri.

Alhaji Isah Muhammad-Musa, kwamishinan ayyuka na musamman, ya yaba da wannan mataki na ƙungiyoyi masu zaman kansu, inda ya ce hakan ya ƙarawa ƙoƙarin Gwamna Dikko wajen tallafawa marasa galihu da marayu a jihar.

Ya bayyana cewa, uwargidan gwamnan ta shirya yin irin wannan aikin na jin ƙai nan ba da jimawa ba, tare da ƙara azama wajen ɗaukaka masu buƙata a cikin al’umma.

Kalli hotona a nan:

Continue Reading

Kungiyoyi

Za a yi taron ƙasashen Musulmai da na Larabawa a Saudiyya kan yaƙin Gaza

Published

on

Saudiyya ta ce za ta karɓi baƙunci taron ƙungiyar Haɗin Kan Ƙasashen Musulmai don tattauna yaƙin Gaza

Ministan zuba jari na ƙasar Saudiyya ya ce, nan da kwanaki masu zuwa ƙasar za ta karɓi baƙuncin taron koli na ƙasashen Larabawa da ƙasashen Musulmai domin tattaunawa kan yaƙin Isra’ila da Falasɗinu.

“Za mu gani a cikin ‘yan kwanaki masu zuwa, Saudiyya ta ƙira wani taron gaggawa na Larabawa a Riyadh,” in ji ministan zuba jari na Saudiyya Khalid Al-Falih, a taron Bloomberg New Economy Forum a Singapore.

KU KUMA KARANTA: An harba rokoki daga Gaza zuwa Tel Aviv

“A cikin kankanin lokaci, makasudin gabatar da waɗannan tarukan guda uku da sauran tarukan ƙarƙashin jagorancin Saudiyya shi ne a kai ga warware rikicin cikin lumana.”

Kamfanin dillancin labaran Etemad ya rawaito cewa, shugaban ƙasar Iran Ibrahim Raisi zai tafi Saudiyya a ranar Lahadi mai zuwa don halartar taron kolin Ƙungiyar Haɗin kan Ƙasashen Musulmai, wadda ita ce ziyarar farko da wani shugaban ƙasar Iran ya kai tun bayan Tehran da Riyadh suka kawo ƙarshen rashin jituwar da aka shafe tsawon shekaru ana yi ƙarƙashin wata yarjejeniya da China ta kulla a watan Maris.

Continue Reading

Jan hankali

Sun yi wa likita dukan kawo wuƙa saboda ‘yar uwarsu ta rasu a Asibiti

Published

on

A ranar Talata ne wani mutum da ɗansa suka fusata inda suka sauke fishin su akan wani babban likita da ma’aikaciyar jinya a cibiyar kiwon lafiya ta tarayya da ke Idi-Aba, Abeokuta bayan da ‘yar uwansu ya rasu a cibiyar.

Rikicin ya ɓarke ne da misalin ƙarfe 2:00 na safiyar ranar Talata, a sashen bayar da agajin gaggawa na asibitin jim kaɗan bayan wata mara lafiya mai shekaru 53 ta rasu.

Shugaban ƙungiyar likitocin Najeriya reshen jihar Ogun, Dakta Kunle Ashimi yayin da yake zantawa da manema labarai, ya yi Allah wadai da harin da ‘yan uwan mamaciyar suka kai wa biyu daga cikin ma’aikatan jinya,akan mutuwar matar a sakamakon ciwon zuciya.

KU KUMA KARANTA:Lauya ya yi wa tsohon mijin wacce yake karewa duka a kotu

Ashimi ya ce Dr Pelumi Somorin likitan ne wanda abin ya shafa,yayin da ba a tantance ko waye ma’aikaciyar jinya ba.

Ya bayyana cewa mahaifin da ɗan, sun mari likitan yayin da aka sanar da su mutuwar yar uwar su.

A cewar Ashimi, matar ‘yar shekara 53 da aka kawo asibitin da ciwon zuciya mai tsanani, wanda ita kanta bayan binciken da ta kawo daga cibiyar da aka turo ta, ya nuna cewa,ba za ta ɗauki fiye da kwana ɗaya ba, sai dai wani ikon Allah.

“Watau ta kasance a matakin ƙarshe na gazawar zuciyarta. An bayyana hakan ga ’yan uwan ta, lokacin da aka kawo ta wurin, amma duk da haka mun yi imanin cewa,Allah kan iya yin wani abu, kuma muna jin cewa ya kamata mu yi iya ƙoƙarinmu don ganin mun taimaka mata.

“Ya taɓa faruwa a baya cewa, wani mutum da ke cikin irin wannan yanayin ya samu sauki tare da kulawar da ta dace.

“Amma abin takaici, wannan majinyaciyar ta mutu da misalin karfe 2 na safe kuma mijin da ɗan marigayiyar suka faɗa kan likitan da ke kula da mara lafiyar lokacin da aka sanar da labarin rasuwarta.

“Sun mari likitan , daga baya kuma suka hau matar mutanen da ke kusa da su suka yi ta jibgarta.

“Waɗannan mutanen kuma sun ci mutuncin wata ma’aikaciyar jinya” in ji shi.

Shugaban ƙungiyar ya ce an sanar da ‘yan sanda game da lamarin, inda ya ƙara da cewa duk da kasancewar ‘yan sanda a wajen,ɗan ya ci gaba da cin mutuncin su.

“An kira ‘yan sanda kuma DPO na ofishin ‘yan sanda na Kempta ya jagoranci tawagar ‘yan sanda zuwa wurin.

“Duk da kasancewar ‘yan sanda, ɗan mamacin ,ya afkawa wata ma’aikaciyar jinya kuma duk ƙoƙarin kwantar da hankalinsa da aka yi, ya ci tura.

“A karshe an kai mutanen biyu zuwa ofishin ‘yan sanda na Kemta, inda aka ɗauki bayanansu da na likitan da aka kai wa harin, ma’aikacin jinya da kuma shaidun da ke kewaye.”

Shugaban na NMA, ya gargadi ‘yan Najeriya da su daina cin zarafin ma’aikatan kiwon lafiya, yana mai shan alwashin cewa, duk wanda aka samu da laifi za a gurfanar da shi a gaban kotu.

“Mun yanke shawarar cewa wannan zai zama na ƙarshe kuma ba za mu yadda a bamu haƙuri ba, mun yanke shawarar mika ƙarar zuwa kotu kuma gobe za mu kasance a kotu.

“An fara duk wata shari’a kuma za mu kai wannan ƙara kotu.

“Muna so mu yi kira da kuma gargaɗi ga duk waɗanda suke zuwa asibitoci a Ogun cewa ƙungiyar likitocin Najeriya, da sauran abokanta da kowane likita, ba za su amince da kalmar “ayi hakuri” nan ba daga yanzu, daga duk wanda ya zagi wani daga cikin membobinmu.

“Za mu yi iya bakin kokarinmu wajen gurfanar da irin waɗannan mutanen kuma ba za mu amince da rokon kowa ba komai girman mutum.

“Don haka, muna rokon duk wanda yake da hankali ya yi tunanin zai iya roƙon mu daga baya don faranta ran jama’a. Ba laifinmu bane”.

Ashimi ya jaddada cewa, cin zarafin ma’aikatan lafiya ya zama ruwan dare gama duniya, wanda har yanzu ba a warware shi ba duk da kamfen da aka yi na daƙile barazanar.

Ya ce “a duniya baki daya, wannan batu ne da ke ci gaba da gudana kuma an gudanar da yakin akan hana hakan, da dama a duk faɗin duniya na yakar tashe-tashen hankula da cin zarafi da ake yi wa ma’aikatan lafiya.

“Musamman a cibiyar kiwon lafiya ta tarayya a Abeokuta, jihar Ogun da sauran asibitocin da ke kewayen Jihar Ogun waɗanda ke ƙarkashin ikonmu a matsayin kungiyar likitocin Najeriya.

“Mun gudanar da yaƙi da hani,da irin halayyar nan, da dama a kan wannan taron a baya kuma bayan yawan rokon da muka yi, sai da muka roƙi likitocinmu da su karɓi uzurin waɗanda suke yin abun

“Abubuwa irin wannan ba sa raguwa, a zahiri, wannan yana faruwa sau da yawa a lokuta da dama.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like