Connect with us

Labari

Idan Ba Mu Dage Da Gaske Ba ISWAP Za Ta Mamaye Najeriya – Zulum

Published

on

Gwamnan jihar Borno Farfesa Babagana Umara Zulum ya nuna “matukar” damuwa kan yadda mayakan ISWAP ke karuwa a wasu sassan jihar, lamarin da ya sa ya yi kira ga jami’an tsaro da su dauki “matakan gaggawa.”

Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin da Kwamitin Majalisar Dattawan Najeriya da ke kula da sha’anin sojin kasar ya ziyarce shi a ranar Laraba a Maiduguri.

“Maganar gaskiya ita ce, ya zama dole mu dauki mataki akan mayakan ISWAP a jihar Borno, idan muka ki fatattakar su, ta yi wu su zama matsala ba ga yankin arewa maso gabas kadai ba, har ma da daukacin Najeriya.”

Kwamitin ya kai ziyarar ne karkashin jagorancin Sanata Mohammed Ali Ndume kamar yadda wata sanarwar da gwamnatin Bornon ta fitar ta ce.

Farfesa Zulum ya kara da cewa, “mayakan ISWAP na da makamai kuma a shirye suke sannan suna da basira fiye da mayakan Boko Haram kuma suna karuwa akai-akai, dalilin kenan da ya sa ya kamata a fatattake su.”

Gwamnan ya kuma mika godiya ga gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari da dakarun Najeriya da masu ayyukan sa-kai saboda irin taimakon da suke bayar wa.

“Jihar Borno na ganin dawowar zaman lafiya a hankali. Hakan ya yi wu ne saboda taimako da gwamnatin tarayya ta ba mu. Sannan shugabannin jami’an tsaro su ma suna ba da nasu hadin kan. A takaice, shugabannin rundunonin soji (GOCs) su ma suna ba da nasu taimakon,” Zulum ya ce.

Sai dai gwamnan ya nuna damuwa kan yadda mayakan ISWAP suke barazanar mayar da hannun agogo baya kan nasarorin da aka samu.

A gefe guda kuma gwamnan har ila yau ya ce mika wuya da daruruwan mayakan Boko Haram suka yi a kwanan nan, ya sa ana samun zaman lafiya musamman a yankunan da ake ayyukan noma.

Gabanin jawabin na gwamna Zulum, Sanata Ndume ya fada cewa kwamitin ya kai ziyarar ne don nuna godiya ga gwamnatin jihar Borno kan yadda take ba sojoji hadin kai da taimako, batun da su ma dakarun kasar suka jaddada a baya.

Newest

Ni ɗan jarida ne mai zaman kansa. Mawallafi kuma mai sharhi a lamarin yau da kullum.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like