Connect with us

Labari

Hukumar Kwastam Shiyyar Kano/Jigawa Ta Kama Fatun Jaki Na Sama Da Miliyan 416

Published

on

Daga; Rabo Haladu, Kaduna.

HUKAMAR Hana Fasa-kwauri ta Kasa shiyyar Kano da Jigawa, ta bayyana cewa ta samu nasarar kama fatun jaki guda 3,712 wanda kudinsu ya kai sama da miliyan 416 da wasu haramtattun kaya.

Shugaban hukumar Kwantirola Mohammed Abubakar Umar, shi ne ya sanar da hakan lokacin da yake baje kolin kayan ga manema labarai a hedkwatar hukumar dake Kano.

Hakazalika, ya kara da cewa hukumar ta tara kudin haraji sama da Naira biliyan 10.1 a cikin watanni uku da ya yi da fara aiki a matsayinsa na Shugaban hukumar a shiyyar Kano da Jigawa.

Kwantirola MA Umar, ya bayyana cewa daga cikin kayayyakin da Hukumar Hana Fasa-kwauri ta shiyar Jihar Kano da Jigawa ta kaman, har da Fatun Jakunkuna da suka kai kimanin guda 3,712 wanda adadin kudinsu ya kai Naira 416,382,278 wanda aka yi kokarinn fita da su zuwa Kasar waje, sai kuma shinkafar waje mai nauyin kilo 50 guda 1,031 da fakitin taliyar waje guda 151 sai fakitin Macaroni guda 91.

Sauran kayan sun hada da, dilar gwanjo guda 131 da kuma shinkafar waje mai kilo 25 guda 3 da kuma sabulun wanki na waje guda fakiti 6.

Acewarsa, daga kama aikinsa zuwa yanzu hukumar ta samu nasarar kara tara kudin harajin da take samu inda ya ce a shekarar data gabata hukumar ta tara biliyan 7 amma daga zuwansa cikin watanni uku sun tara Naira biliyan 10 da doriya.

MA Umar, ya kara da cewa zasu ci gaba da lalubo hanyar da zasu kara inganta samun kudadan haraji ta hanyar yin aiki kafada da kafada da sauran bangarorin hukumar dake aiki a shiyyar.

Ya ce hakan ya samu ne bisa irin kwarin gwiwar da shugaban hukumar kwastan ta kasa Hameed Ali yake basu ne, yana mai cewa za su ci gaba da yin bakin kokarin su wajen tabbatar da cewa an hana fasa kwauri domin bunkasa ci gaba tattalin arzikin Najeriya baki daya.

Ya kara da cewa hukumar kwastan shiyyar Kano da Jigawa, ta himmatu wajen ganin ta dakile ayyukan masu fasa kwauri inda yace Jami’ansu suna aiki babu dare babu rana domin tabbatar da hakan.

Ya ce “za mu yi bakin kokarin mu wajen ganin munyi aiki da masu ruwa da tsaki a shiyyar wajen ganin hakarmu ta cimma ruwa akan samar da hanyoyin bunkasa ci gaban tattalin arzikin kasa baki daya.”

A karshe, Kwantirolan ya yi kira ga ‘yan Najeriya da su rika kiyaye doka, domin ko kadan bai kamata a ci gaba da shigo da ire-iren wadannan kayayyaki da aka san gwamnati ta haramta shigowa da su ba.

Ni ɗan jarida ne mai zaman kansa. Mawallafi kuma mai sharhi a lamarin yau da kullum.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like