Connect with us

Labari

Dattijo Ya Yi Allah-Wadai Da Hare-Haren ‘Yan Ta’adda A Kaduna

Published

on

…Ya Dakatar Da Shirin Tuntuba Tare Da Bayar Da Tallafi Ga Wadanda Abin Ya Shafa

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

DAYA daga cikin jiga-jigan ‘yan takarar Gwamna a Jam’iyyar APC a Jihar Kaduna, Muhammad Sani Abdullahi (Dattijo), ya bayyana bakin cikinsa bisa ga samun labari mai ban tausayi na harin Jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna, kana da sauran hare-haren yan ta’adda da aka kai a garin Kaura, Jema’a da Giwa da ya yi sanadiyar rasa rayuka a yan kwanakin nan.

A wata sanarwa da ya raba wa manema labarai kuma mai dauke da sa hannunsa da kansa, Dattijo ya yi Allah-Wadai da hare-haren tare da jajantawa wadanda harin ya rutsa da su da iyalansu kan harin da aka kai.

Sanarwar ta ruwaito Dattijo yana cewa; “Na yi matukar bakin ciki da harin jirgin kasa da ‘yan ta’adda suka kai a ranar litinin da yammah. Tunanina da addu’o’i suna tare da wadanda abin ya shafa da kuma iyalansu kan abin bakin ciki na lamarin daya faru”.

Dattijo ya kuma jajanta wa Gwamna Nasir Ahmad El-Rufai, iyalai da masoyan wadanda harin jirgin kasan Kaduna, Kaura/Jema’a da Giwa ya rutsa da su tare da addu’ar Allah ya jikan wadanda suka rasu sakamakon harin, da yin addu’ar samun lafiya ga wadanda suka jikkata.

“Ina mika ta’aziyyata ga babanmu kuma shugabanmu, Malam Nasir El-Rufai, iyalai da wadanda harin ya shafa.” Dattijo ya ce.

Dattijo ya kuma yabawa jami’an tsaro bisa ga kokarin da suka yi na kai dauki da irin kwarewarsu, sannan ya bukace su da su karfafa aikin hadin gwiwa domin tabbatar da samun nasara a bisa tsarin da Gwamnatin El-Rufai ta yi a fannin tsaro.

“Aikin hadin gwiwa domin ayyukan ceto abin yabawa ne amma ina kira da a samar da hadin kai tsakanin Jami’an tsaro domin samun nasarori a tsarin hada hannu da karfe da gwamnatin Jihar Kaduna ke shiryawa a fannin tsaro domin dakile duk wasu ayyukan ta’addanci a Jihar,” in ji Dattijo.

“A halin da ake ciki, an dakatar da duk wasu ayyuka Kamfen dina da aka shirya a ci gaba da rangadin karamar hukumar da tuntuba na neman tsayawa takara har sai wani lokaci.”

Sanarwar ta kuma sanar da bayar da gudummawar da ba a bayyana adadinsu ba ga wadanda harin ya rutsa da su.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like