Connect with us

Labari

Harin Jirgin Kasa: Uba Sani Ya Nemi Hukumomin Tsaro Su Gaggauta Sauya Dabaru

Published

on

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

SANATA mai wakiltar Shiyyar Kaduna ta tsakiya Malam Uba Sani, ya yi kira ga hukumomin tsaro da abin ya shafa da su gaggauta sauya dabaru domin yakar ta’addanci, ‘yan fashi da sauran matsalolin rashin tsaro a fadin Najeriya, musamman a Jihar Kaduna.

A wani kudiri da aka gabatar a Majalisar Dattawan game da harin da aka kai a daren Litinin wanda ya jawo cece-kuce, Sanatan mai wakiltar Shiyyar Kaduna ta tsakiya ya bayar da umarni na 41 da 51 da suka dace da neman izinin majalisar dattawa ta gabatar da kudiri kan hare-haren ‘yan bindiga dake hanyar Abuja-Kaduna da kuma wasu sassan Jihar.

Dan takarar Gwamnan Kaduna a zaben 2023 mai gabatowa ya koka da yawaitar hare-haren da ake kaiwa kauyukan da ba su jin dadin ganin hakan, wadanda ya ce al’ummar suna fuskantar azabar da ba za a iya misalta su ba, hasarar rayuka da ababen more rayuwa.

Ya bayyana cewa an kashe sama da mutane 50 tare da yin garkuwa da wasu 100 a cikin kwanaki uku a kauyukan da ke fadin kananan hukumomin Igabi da Giwa wanda ya ce sun wani yanki ne a mazabar sa na shiyyar Kaduna ta tsakiya.

Sanatan ya ce a tunaninsa idan aka ayyana ‘yan bindiga a matsayin ‘yan ta’adda zaman lafiya zai dawo, amma abin takaici, ya koka da cewa sabanin yadda lamarin ya kasance na ta’addanci – abubuwan da ke da alaka da su da suka yi sanadin asarar rayuka da kuma kara yawan ‘yan gudun hijira.

Ya yi mamakin yadda mutum mai hankali zai dana nakiya a jirgin fasinjoji su kama harba harsasai a cikin mutane, ciki har da mata da yara da kuma sace wasu dari ba tare da tausayi ba.

Sanatan ya kalubalanci hukumomin tsaro da su dauki ingantacciyar hanyar yaki da ta’addanci ba ta hanyoyin da aka saba amfani da su ba, inda ya bayyana cewa dole ne a dakatar da asarar rayuka ta hanyar da ta dace ta yadda ‘yan Najeriya za su rika tafiye-tafiye da gudanar da sana’o’insu na halal ba tare da tsoro ko tsangwama ba.

Ya jajantawa iyalan wadanda suka rasa rayukansu, yana mai rokon Allah ya jikan su kuma yi addu’ar Allah ya bayyana wadanda aka sace cikin gaggawa.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like