Connect with us

Siyasa

An Buƙaci El-Rufa’i Da Bayar Da Takarar Gwamna A Jam’iyyar APC Ga ‘Yan Shiyya Ta Daya

Published

on

Daga; USMAN NASIDI Da Mustapha Imrana, Kaduna.

WASU masu ruwa da tsaki na Jam’iyyar APC da suka fito daga shiyyar ta daya a Jihar Kaduna sun roki Gwamna Nasir El-Rufa’i da ya ba shiyyar damar fitar da dan takarar Kujerar Gwamnan Jihar a karkashin Jam’iyyar APC a zabe mai zuwa domin yin gaskiya da adalci.

A cewarsu, an mayar da yankin saniyar ware idan ana maganar nade-nade duk da irin gudunmawar da suke baiwa Jam’iyyar da Jihar.

A wani taron manema labarai da suka gudanar a sakatariyar kungiyar ‘yan Jaridu ta Najeriya (NUJ) reshen Jihar Kaduna a ranar Litinin da ta gabata, wanda Ahmed Yahaya Lere da Usman Ahmed Danbaba suka yi jawabi a madadin masu ruwa da tsaki na shiyyar, sun bayyana cewa shiyyar su ce kashin bayan Jam’iyyar APC a Jihar Kaduna.

Sun ce “Hakika muna godiya bisa irin yadda Gwamnatin Jihar Kaduna ke yin ayyuka a ko’ina a duk fadin Jihar Kaduna da nufin kara inganta rayuwar al’umma baki daya, kuma hakan duk ya samu ne sakamakon irin cikakken hadin kai da goyon bayan da mutanen yankin shiyya ta daya suka dade su na bayarwa ga tafiyar wannan Gwamnatin APC”.

“Kowa ya sani cewa shiyyar mu ce ta fi karfi a Jihar, hakan ya faru ne saboda babu shakka ayyukanmu na ci gaba da yin fice a duk zabukan da suka gabata na 2015 da 2019 da kuma zabukan kananan hukumomi da aka yi kwanan nan.

“Wasu daga cikinmu a nan mun kasance shugabannin Jam’iyyar na Jiha da na shiyya, wakilan Jam’iyyar da suka dawo gida, tsofaffin Jami’an Gwamnati da ’yan takara, amma abin da ya fi muhimmanci shi ne, mun damu matuka da makomar Jam’iyyar tare da karfafa nasarorin da Gwamnatin Mallam Nasir Ahmad El-Rufa’i ta samu.

“Bayan doguwar tattaunawa da tuntubar juna a madadin jama’armu, mun bayar da kwarin gwiwa wajen neman wadannan abubuwa kan zaben wanda zai gaji shugabanmu, Malam Nasir El-Rufai.

Acewarsu, sun yi iƙirarin cewa suna da bukatar gwamna mai zuwa ya fito daga shiyyar saboda dalilai kamar haka.

Misali shiyya ta daya tana da Sanata, ‘yan majalisar wakilai shida, ‘yan majalisar dokokin waje goma sha daya, shugabannin kansiloli bakwai duk daga shiyyar ne.

Sai dai sun koka da cewa babu wani daya daga cikinsu a matsayin Gwamna, Mataimakin Gwamna, Ministoci biyu, Shugaban Jam’iyya, Sakataren Jam’iyya, Shugaban Mata, Shugaban Matasa ko kuma Wakilin Jiha a Jam’iyyar APC ta kasa daga shiyyar.

Sun kara da fayyace cewa su na sa ne fa yawan kuri’un da ake samu daga wasu yankuna a jam’iyyar APC raguwa kawai yake yi a koda yaushe, ” Amma yawan kuri’un da APC ke samu a yankin shiyya ta daya karuwa kawai abin yake kuma hakan a bayya ne yake, har ma karamar hukumar Zariya ita ta fi kowace karamar hukuma a Najeriya ba shugaba Bubari kuri’a a zaben da ya gabata ga dai misalai nan da yawa na cancantar kujerar Gwamna a APC sai shiyya ta daya.

Domin karfafawa da ci gaba da ayyukan yaba wa Gwamna a ‘yan kwanakin nan, ana bukatar dan takara wanda ya kware, mai taka rawar gani da kuma sanin tsare-tsare na gwamnatin Mal. Nasiru El-Rufai.

Ni ɗan jarida ne mai zaman kansa. Mawallafi kuma mai sharhi a lamarin yau da kullum.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Siyasa

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Published

on

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Jam’iyyar APC reshen Jihar Zamfara ta dakatar da Ɗan Majalisar Wakilai, Aminu Jaji bisa wasu zarge-zargen da ake yi masa na cin amanar jam’iyyar.

Sakataren Yaɗa Labarai na Jam’iyyar APC na Jihar, Malam Yusuf Idris ne ya sanar da dakatarwar a wani taron manema labarai a Gusau a ranar Juma’a.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa, Jaji yana wakiltar mazaɓar Ƙaura-Namoda/Birnin-Magaji a Majalisar Wakilai a ƙarƙashin jam’iyyar APC.

Idris ya ce wasu zarge-zargen da ake yi wa Ɗan Majalisar sun haɗa da aikata rashin gaskiya da rashin zuwa tarurrukan jam’iyyar da kuma sauran ayyuka.

KU KUMA KARANTA: Kotun Najeriya ta bayar da umarnin dakatar da asusun banki fiye da dubu 1

Ya ce, matakin ya biyo bayan sanarwar dakatarwar da aka yi wa Jaji daga shugabannin jam’iyyar APC na mazaɓar Birnin-Magaji bisa zargin cin amanar jam’iyyar da dai sauran abubuwan da suka saɓa wa jam’iyyar.
Idris ya ce, “Kwamitin zartaswa na jam’iyyar APC na ƙaramar hukumar Birnin Magaji ne ya miƙa sanarwar dakatarwar zuwa hedikwatar jam’iyyar APC ta jihar.

Bayanai sun ce kwamitin zartaswar jam’iyyar APC na jihar ya gudanar da taron gaggawa a sakatariyar jam’iyyar da ke Gusau a ranar Juma’a 17 ga watan Mayu, 2024, inda aka gabatar da batun dakatar da Jaji ga ‘yan majalisar zartarwar jihar.

Continue Reading

Labarai

Tsohon gwamnan Katsina, Shema ya sauya sheƙa zuwa APC

Published

on

Tsohon gwamnan jihar Katsina, Ibrahim Shema, a hukumance ya koma jam’iyyar APC Mai mulki a jihar.

Shema, ya kasance gwamnan jihar a tsakanin shekarar 2007 zuwa 2015, a ƙarƙashin jam’iyyar PDP.

Tsohon gwamnan ya yi rajista ne a ofishin jam’iyyar na mazaɓar Shema, ƙaramar hukumar Dutsin-ma, inda shugaban jam’iyyar na jihar, Sani Aliyu-Daura ya ba shi katin zama ɗan jam’iyyar APC.

Lambar katin Shema ta zama ɗan jam’iyyar ita ce: 26551.

KU KUMA KARANTA:Gwamnatin Yobe za ta mayar da kwale-kwalen Dufuna mai shekaru 8,000 zuwa cibiyar yawon buɗe ido

Malam Aliyu-Daura ya yabawa Gwamna Dikko Raɗɗa da kuma tsohon gwamnan jihar Aminu Masari wanda ya gada, a bisa rawar da suka taka wajen ganin Shema ya sauya sheƙa.

Don haka ya tabbatar wa tsohon gwamnan cewa za a yi masa adalci kamar kowane ɗan jam’iyya.

Shugaban ma’aikata na Raɗɗa, Jabiru Abdullahi-Tasuri, shi ne ya miƙa katin zama ɗan jam’iyya ga Shema a madadin gwamnan a jiya Alhamis a Dutsin-ma.

Continue Reading

Labarai

Fusatattun matasa sun lakaɗawa kwamishina duka a wajen zaɓen fidda gwani

Published

on

Banji Ajaka, kwamishinan lafiya na jihar Ondo, ya gamu da fushin matasa a jiya Asabar yayin da ake gudanar da zaɓen fidda gwani na gwamna na jam’iyyar APC mai mulki a jihar.

Daily Trust ta gano cewa Dakta Ajaka, wanda ke Mazaɓar Ugbo 3, a ƙaramar hukumar, ana zarginsa da ɓoye takardar sakamakon zaɓen.

Shaidu sun tabbatar da faruwar lamarin a wata tattaunawa da suka yi da manema labarai, inda suka yi zargin cewa fusatattaun matasan ‘ya’yan jam’iyyar APC ne da ke adawa da tsarin da aka bi wajen gudanar da zaɓen.

Ɗaya daga cikin waɗanda suka shaida lamarin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana cewa rikicin ya faro ne lokacin da ‘yan ɗaya ɓangaren na jam’iyyar suka buƙaci ganin takardar sakamakon zaɓen na fidda gwani.

KU KUMA KARANTA:An yi jana’izar tsohon gwamnan Ondo, Rotimi Akeredolu

“Sun fusata ne suka buƙaci jami’in zaɓe ya ba su takardar sakamakon zaɓen sai kuwa ya ce ta na wajen Ajaka.

“Don haka suka yi masa duka a wurin, inda kuma garinsu ne. Jama’a sun fusata sosai da lamarin, inda rigimar ta ƙare a wajen.”

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Dakta Ajaka ya ce an zarge shi ne da riƙe takardar sakamakon zaɓen.

Ya yi bayanin cewa a lokacin da yake ƙoƙarin bayyana kansa, ’yan daban sun auka masa inda suka yi masa mugun duka.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like