Connect with us

Siyasa

Haruna AG, Ya Koma Jam’iyyar PDP Domin Yin Takarar Gwamnan Kaduna

Published

on

Daga; USMAN NASIDI Da MUSTAPHA IMRANA, Kaduna.

TSOHON Dan takarar Kujerar Gwamnan Jihar Kaduna a Jam’iyyar CPC, APC da SDP wanda yake tsohon babban akanta Janar Gwamnatin Jihar da ya fi kowanne dadewa a kan mukamin, Alhaji Dokta Haruna Yunusa Saeed Kajuru, ya sauya sheka ta hanyar komawa Jam’iyyar PDP.

Dan takarar Kujerar Gwamnan Jihar, ya bayyana kudirinsa ne a yayin wani gangamin komawarsa Jam’iyyar PDP wacce ya bayyana a matsayin gida da kuma bayyana ra’ayinsa na tsaya takarar neman Kujerar Gwamnan Jihar Kaduna a ranar talata a sakatariyar Jam’iyyar da ke NDA Kaduna.

Da yake jawabi a wajen taron, Haruna Saeed (AG), ya bayyana cancanta, kokari, iya aiki da sanin ciki da wajen Jihar a matsayin ma’aunin da za a yi amfani da shi wajen zabe shi a matsayin dan takarar Kujerar Gwamnan Jihar.

Ya ce “kamar yadda na Sani ni ne a kan gaba wajen ganin Jam’iyyar APC ta Kafu sosai a Jihar Kaduna, har aka samu nasarar da ake takama da ita a yanzu amma kuma bisa wadansu dalilai a halin yanzu na koma asalin gidana na wacce ta ke PDP wanda tare da ni aka kafa ta kuma ba rike mukamai tare da yin ayyukan ci gaban rayuwar Jama’a da dama a cikin ta”.

“Ni ne ma’aikacin da ya fi kowa dadewa a kan kujerar babban akanta Janar a Jihar Kaduna domin na shekara Goma sha daya (11) da ba a ta ba samun wanda ya samu damar yin hakan ba, na kuma yi aikin karantarwa tun daga Firamare, sakandare zuwa Jami’a na yi aikace-aikace da dama da suka hada da shugaban kamfanin zuba jari da hukumar NAITI inda na zama shugaba baki daya a Najeriya”.

Ni ne dai wanda aka Sani ina nan ban canza ba sai ci gaban da na yi, kuma na gina makarantar sakandare tun daga matakin aji uku zuwa babbar sakandare na ba Gwamnati kyauta na kuma gina makarantun Islamiyya da masallatai duk domin taimakawa bayin Allah.

Acewarsa, ko a halin yanzu da akwai abubuwa da dama da zai yi wa Jihar Kaduna domin a samu ci gaban da kowa ke bukatar samu don su ke da masaniya a kan wurare da dama wadanda suka hada da lunguna-lunguna a cikin birane da karkara.

Hakazalika, ya koka bisa irin yadda Gwamnatin Jihar Kaduna ke aikin tituna a garin Kaduna da kuma yan kadan a Zariya da Kafanchan wanda hakan da sauran abin dubawa domin kamar shi da ya fito daga kauye har yanzu su na jiran ayi masu aiki, domin tun daga Gwantu zuwa Fala zuwa yankin Dogon Dawa har karshen birnin Gwari a Jihar Kaduna duk ko’ina sun san haka, balantana shi da ya yi aiki a matsayin makogwaron Jihar Kaduna ta fuskar kudi wadda kowace ma’aikata sai ta zo ofishinsa.

Yayin da mayar da martani ga Dan takarar, Shugaban Jam’iyyar PDP na Jihar Mista Felix Hassan Hyet, ya bayyana Jindadinsu bisa ganin tsohon dan Jam’iyyar da magoya bayansa sun yi mubayi’a, kana sun dawo Jam’iyyar ta su ta PDP wacce ya bayyana a matsayin mai albarka da nasara.

Shugaban ya kara da cewa yin hakan na nuni da cewa wata dama ce a gare da zasu iya samun nasarar kwace duk wasu kujeru daga hannun Jam’iyyar adawa mai mulki idan har sun yi dacen samun mutane yan takara na gari, ko da ita Jam’iyyar PDP ba zata yiwa kowa karfa-karfa ba face sai abin da mutane suka zaba yayin zaben fidda gwani.

A karshe, ya shawarci Haruna Saeed (AG) da sauran yan takarar da su san cewa Mulkin na Allah ne kuma su san irin kalaman da zasu rika amfani da su domin sun zama majibantan yan uwan juna saboda haka kowani Dan takara ya yi kokarin ganin cewa ya kiyaye duk wani abun da zai haifar da wata matsala.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Siyasa

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Published

on

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Jam’iyyar APC reshen Jihar Zamfara ta dakatar da Ɗan Majalisar Wakilai, Aminu Jaji bisa wasu zarge-zargen da ake yi masa na cin amanar jam’iyyar.

Sakataren Yaɗa Labarai na Jam’iyyar APC na Jihar, Malam Yusuf Idris ne ya sanar da dakatarwar a wani taron manema labarai a Gusau a ranar Juma’a.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa, Jaji yana wakiltar mazaɓar Ƙaura-Namoda/Birnin-Magaji a Majalisar Wakilai a ƙarƙashin jam’iyyar APC.

Idris ya ce wasu zarge-zargen da ake yi wa Ɗan Majalisar sun haɗa da aikata rashin gaskiya da rashin zuwa tarurrukan jam’iyyar da kuma sauran ayyuka.

KU KUMA KARANTA: Kotun Najeriya ta bayar da umarnin dakatar da asusun banki fiye da dubu 1

Ya ce, matakin ya biyo bayan sanarwar dakatarwar da aka yi wa Jaji daga shugabannin jam’iyyar APC na mazaɓar Birnin-Magaji bisa zargin cin amanar jam’iyyar da dai sauran abubuwan da suka saɓa wa jam’iyyar.
Idris ya ce, “Kwamitin zartaswa na jam’iyyar APC na ƙaramar hukumar Birnin Magaji ne ya miƙa sanarwar dakatarwar zuwa hedikwatar jam’iyyar APC ta jihar.

Bayanai sun ce kwamitin zartaswar jam’iyyar APC na jihar ya gudanar da taron gaggawa a sakatariyar jam’iyyar da ke Gusau a ranar Juma’a 17 ga watan Mayu, 2024, inda aka gabatar da batun dakatar da Jaji ga ‘yan majalisar zartarwar jihar.

Continue Reading

Labarai

Tsohon gwamnan Katsina, Shema ya sauya sheƙa zuwa APC

Published

on

Tsohon gwamnan jihar Katsina, Ibrahim Shema, a hukumance ya koma jam’iyyar APC Mai mulki a jihar.

Shema, ya kasance gwamnan jihar a tsakanin shekarar 2007 zuwa 2015, a ƙarƙashin jam’iyyar PDP.

Tsohon gwamnan ya yi rajista ne a ofishin jam’iyyar na mazaɓar Shema, ƙaramar hukumar Dutsin-ma, inda shugaban jam’iyyar na jihar, Sani Aliyu-Daura ya ba shi katin zama ɗan jam’iyyar APC.

Lambar katin Shema ta zama ɗan jam’iyyar ita ce: 26551.

KU KUMA KARANTA:Gwamnatin Yobe za ta mayar da kwale-kwalen Dufuna mai shekaru 8,000 zuwa cibiyar yawon buɗe ido

Malam Aliyu-Daura ya yabawa Gwamna Dikko Raɗɗa da kuma tsohon gwamnan jihar Aminu Masari wanda ya gada, a bisa rawar da suka taka wajen ganin Shema ya sauya sheƙa.

Don haka ya tabbatar wa tsohon gwamnan cewa za a yi masa adalci kamar kowane ɗan jam’iyya.

Shugaban ma’aikata na Raɗɗa, Jabiru Abdullahi-Tasuri, shi ne ya miƙa katin zama ɗan jam’iyya ga Shema a madadin gwamnan a jiya Alhamis a Dutsin-ma.

Continue Reading

Labarai

Fusatattun matasa sun lakaɗawa kwamishina duka a wajen zaɓen fidda gwani

Published

on

Banji Ajaka, kwamishinan lafiya na jihar Ondo, ya gamu da fushin matasa a jiya Asabar yayin da ake gudanar da zaɓen fidda gwani na gwamna na jam’iyyar APC mai mulki a jihar.

Daily Trust ta gano cewa Dakta Ajaka, wanda ke Mazaɓar Ugbo 3, a ƙaramar hukumar, ana zarginsa da ɓoye takardar sakamakon zaɓen.

Shaidu sun tabbatar da faruwar lamarin a wata tattaunawa da suka yi da manema labarai, inda suka yi zargin cewa fusatattaun matasan ‘ya’yan jam’iyyar APC ne da ke adawa da tsarin da aka bi wajen gudanar da zaɓen.

Ɗaya daga cikin waɗanda suka shaida lamarin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana cewa rikicin ya faro ne lokacin da ‘yan ɗaya ɓangaren na jam’iyyar suka buƙaci ganin takardar sakamakon zaɓen na fidda gwani.

KU KUMA KARANTA:An yi jana’izar tsohon gwamnan Ondo, Rotimi Akeredolu

“Sun fusata ne suka buƙaci jami’in zaɓe ya ba su takardar sakamakon zaɓen sai kuwa ya ce ta na wajen Ajaka.

“Don haka suka yi masa duka a wurin, inda kuma garinsu ne. Jama’a sun fusata sosai da lamarin, inda rigimar ta ƙare a wajen.”

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Dakta Ajaka ya ce an zarge shi ne da riƙe takardar sakamakon zaɓen.

Ya yi bayanin cewa a lokacin da yake ƙoƙarin bayyana kansa, ’yan daban sun auka masa inda suka yi masa mugun duka.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like