Connect with us

Labari

Akwai Bukatar Yin Gyararraki Kusan 30 Zuwa 40 A Kundin Tsarin Mulkin Najeriya – Hon Auwal Jatau

Published

on

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

DAN Majalisar Tarayya mai wakiltar mazabar Zaki ta Jihar Bauchi, Honarabul Auwal Mohammed Jatau, ya bayyana cewa da akwai bukatar yin wasu yan gyare-gyare akalla kusan wurare talatin zuwa arba’in a Kudin tsarin mulkin kasar Najeriya wanda dama wasu al’umma masu sukar ke ganin cewa basu dace da tsarin mulkin Demokoradiyya ba.

Honarabul Auwal Jatau, ya bayyana hakan ne a wani zantawarsa da manema labarai inda ya bayyana cewa wannan wani abu ne wanda dama wasu al’umma sun jima suna sukar al’amuran, kana su karan kansu a matsayin wata kwamitin Majalisar Tarayyar sun tabbatar da hakan.

Ya kara da cewa a bisa yunkurin da suka yi domin gano wasu abubuwan da suke da bukatar sauyin, sun fahimci cewa da akwai wasu sassan dake da bukatar sauyin domin mayar da su ta fuskar Demokoradiyya wacce a kan wannan tafarkin ake tafiya a wannan zamanin.

Ya ce “a Kundin Tsarin Mulkin Kasar nan wadda a yau Najeriya ta ke amfani da shi wajen gabatar da tsare-tsare na mulki, an dade ana sukar wasu gabobi daban-daban na wannan kundi da cewa ya kamata ace an canza su, domin masu sukar suna cewa tsari ne wanda Sojoji su ka yi shi domin biyan wasu bukatun kansu a lokacin da suka samu kansu a madafun iko saboda haka bai yi daidai da tsarin mulkin Demokoradiyya da ake tafiya da ita a yau ba.”

“Wadannan abubuwan a kwamitance, mun zauna mun duba abubuwan da wurare daban-daban wanda daga kan abubuwan da suka shafi masu Sarautun Gargajiya da matsayinsu a kasar da kundin tsarin mulki, matsayin harkokin mata da yara, matsayin harkokin Zabe, matsayin mallakar dukiyar data fito daga karkashin kasa kamar ma’adinai irinsu zinari da dai sauran wasu abubuwan masu mahimmanci da ya kamaci ace an sauya musu fasali.”

“Mun zauna, mun aminta da yin wasu yan gyare-gyaren wanda zaman har ya hada da yan Majalisar Dattawa, kana a zaman da muka yi dasu, mun samu fahimtar juna domin samun sauyi a wadannan a kan abubuwan da suke da bukatar sauyi wajen aiwatar da su a matsayin Kundin Tsarin Mulkin a karkashin mulkin Demokoradiyya.”

Da yake tsokaci bisa ziyarar bazata wacce Uwar-gidan shugaban kasa Hajiya Aisha Buhari ta kaiwa Majalisar, Honarabul Auwal Jatau ya danganta zuwan na ta bisa kudirin ganin cewa an baiwa fannin mata da yara fifiko wanda hakan na daya daga cikin gyare-gyaren da suke da bukatar yi domin samun sauyi a kundin tsarin mulki na kasar.

Acewar mamba na kwamitin gyaran Kundin Tsarin Mulkin Najeriya, da akwai wasu Kungiyoyi na mata na duniya dana Najeriya wanda suke ganin cewa kason da mata suke samu a hidindimu na Najeriya bai yi musu ba ko ya yi musu kadan, saboda haka a kullum bukatar su shi ne a kara musu wani kaso, wanda a bisa irin wadannan dalilai ne yasa ita Uwar-gidan shugaban Kasa da minista suka kawo musu ziyarar zuwa zauren Majalisar Tarayyar domin wasu biyan bukatunsu na mata da kuma yara.

A karshe, Dan Majalisar Tarayyar mai wakiltar mazabar Zaki ta Jihar Bauchi, Honarabul Auwal Mohammed Jatau, ya bada tabbacin cewa Majalisar Tarayyar na Kokarin ganin cewa an samu wannan sauyin domin sun riga sun gabatar da wannan kudiri a Majalisar, illa lokacin kawai suke jira na ganin cewa an samu tabbacin wadannan abubuwan.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like