Connect with us

Labari

Za Mu Yi Kokarin Kare Rayukan Yan Najeriya Dake Ko’ina A Duniya – Hon Munir Lere

Published

on

Daga; BASHIR BELLO, Majalisa Abuja.

DAN Majalisa mai wakiltar mazabar Lere ta Jihar Kaduna a Tarayyar Najeriya, Honarabul, Injiniya Ahmed Munir, ya ba da tabbacin cewa hakkinsu ne tabbatar da kare rayuka da lafiyar duk wasu yan Najeriya a duk fadin duniya, musamman a cikin irin wannan yanayin wanda wasu suka tsinci kansu na halin tashin hankali a kasar Rasha da Ukraine.

Injiniya Ahmed Munir a wata hirarsa da manema labarai jim kadan bayan zaman tattaunawar Majalisar Inda suka mika wani kudirin neman mafita na gaugawa ga al’ummar Kasar da ke cikin wani halin ha’ula’i sakamakon rikicin daya barke a kasashen biyu na Rasha da Ukraine, ya bayar da tabbacin cewa Gwamnatin Najeriya za ta kaiwa al’ummar dake zaune a kasashen dauki na gaugawa.

Ya kara da cewa, a bisa yunkurin da kudirin da suka gabatar yake na ganin cewa an samu mafita ga al’ummar da abun ya shafa, Majalisar Tarayyar ta amince da daukar matakai na gaugawa, kana da bada umarnin kwasho al’ummar da suke zauna a cikin kasashen biyu da lamarin ya shafa domin tabbatar da an kare lafiyarsu da rayuwarsu.

Ya ce “a matsayinmu na yan Majalisu, alkawarin da muka dauka shi ne ko’ina dan Najeriya yake za mu yi kokarin tabbatar da basa cikin wani hadari, don haka muna sane cewa akwai rikici na yaki dake faruwa tsakanin Kasar Rasha da Ukraine a yanzu haka, saboda haka ya zama wajibi mu kare rayuka da lafiyar yan Kasarmu a duk inda suke.”

“Bayan haka ma, ana sane cewa muna da dalibai da dama daga ko’ina a fadin Tarayyar Najeriya da suke karatun Koyon aikin likitanci da sauran darussa da suke chan Kasashen, saboda haka wajibi ne a kare lafiyarsu ta hanyar samun yadda za a fitar da su daga cikin wannan hadarin da suke fuskanta wanda hakan yasa muka gabatar da wannan kudirin a yau.”

“Sai kuma abu na biyu na aikin dake gabanmu shi ne ba wai yin bayanin ne kawai ba face daukar matakin gaugawa wanda hakan yasa kakakin Majalisar ya kara bada tabbaci akai domin a samu Jiragen da za su je su kwaso wadannan mutanen da hadin gwiwar Gwamnatin Tarayyar ta hanyar hukumar harkokin kasashen waje da ya zama wajibi su kula da duk wasu harkokin.”- Inji Shi

Acewarsa, duk wasu ka’idodin da matakan da ya kamaci Majalisar ta bi ko ta dauka domin tabbatar an aiwatar aikin da duk hanyoyin da za a bi domin a samu damar tsaratar da al’ummar Kasar Najeriyan dake kasashen biyu, a yanzu sun riga sun kammala wannan shirin, face illa Gwamnatin Tarayyar kadai suke jira domin ta bada umarnin fara aiwatar da ayyukan domin a kwaso al’ummar.

Har’ila yau, Dan Majalisar Tarayyar mai wakiltar mazabar Lere, ya kara da bada tabbacin cewa baya ga Kokarin ganin an tseratar da al’ummar da ke kasashen, Majalisar za ta yi duba a kan al’amuran da suka shafi sakala daliban da harkokin karatun su zai tsaya a wasu wajajen da suka dace sakamakon matsalar da aka samu don ganin cewa karatunsu bai tsaya ba bayan kwaso su da za ayi.

Daga karshe, Honarabul, Injiniya Ahmed Munir, ya shawarci yan Najeriya dake da yan Uwa a kasashen da abun ya shafa da su kwantar da hankalinsu, kana su ci gaba da yin addu’a domin ganin cewa an samu cin nasarar tsaratar da duka al’ummar Kasar dake kasashen biyu.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like