Connect with us

Labari

Abubuwan Da Ke Faruwa Sun Sabawa Hankali Da Tunani – Honarabul Yusuf Bala

Published

on

Daga; MUSTAPHA IMRANA ABDULLAHI.

WANI Dan takarar Gwamnan Jihar Kaduna honarabul Yusuf Bala Ikara, bayyana abubuwan da ke faruwa sakamakon matsalolin tsaro da cewa sun sabawa Tunani da hankali.

Dan takarar Gwamnan Jihar Kaduna karkashin tutar jam’iyyar APC Yusuf Bala Ikara, ya bayyana hakan a lokacin wata tattaunawa da wakilin mu a Kaduna.

Ya ce “hakika duk mai hankali da basira babu abin da ya dace ya ce sai ‘innalillahi wa’inna ilaihirraji’un’ domin kuwa lamarin da ke faruwa ya sabawa hankali da tunani baki daya, kuma wani lamari ne na bakin ciki da damuwa musamman ga al’ummar wannan yanki, yadda wadannan abubuwa kullum sai ci gaba kawai suke yi.”

“Na farko dai, mu ci gaba da yin addu’a kuma mu koma zuwa ga Allah, na biyu kuma ina yin jaje ga al’ummar Jihar Kaduna musamman na ganin yadda lamarin ya faru, ina mai jajantawa shugaban kasa da wadanda abin ya rutsa da iyalansu kuma ina mai jaje ga al’ummar karamar hukumar Giwa saboda abin ya faru da su har mutane suka rasa rayuka da dama da fatan Allah ya kawo karshe wannan lamarin, kasancewar kusan komai na kara ta’azzara ne a yanzu.”

Ya kara da cewa, abubuwan da ke faruwa ba za mu zargi kowa ba illa dai idan abu yazo a haka, ya dace daga bangaren Gwamnati ta zama ta na magance abu kafin faruwarsa ba wai sai ya faru ace za a dauki mataki ba, kullum akwai mutanen jami’an tsaro na ciki da na bayya ne su na ayyukansu ba mun Raina masu ba ne amma dai su kara kokari.

“Ya dace a fili ace Gwamnati na da labarin faruwar irin wadannan abubuwan a kuma dauki matakan magance su amma ban san abin da ke faruwa ba, amma a dan sanin da na yi kamata ace Gwamnati na da hanyoyin da za ta ji ba wai ayi irin wannan shirin ba amma Gwamnati ba ta Sani ba” a kai hari a harbi mutane a kwashi wasu duk ayi abin da aka yi amma Gwamnati ba ta da hanyar jin wannan labarin a gaskiya ya dace Gwamnati ta sake Daura dammara. Saboda daya daga cikin irin abin da ya sa mutane suka zabi wannan Gwamnatin ke nan ana ganin Gwamnatin baya ta gaza to, muma ta mu gashi ta zo muna yi wa Allah godiya ana bakin kokari amma dai a kara zage damtse, a mike tsaye a kara kokari a kan wannan lamarin.” Inji Shi

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like