Connect with us

Siyasa

‘Yan Majalisar Dokoki Ba Su Yi Amfani Da Dattako Wajen Fuskantar Koke Koken Mata Ba – Aisha Buhari

Published

on

Daga Wakilinmu.

UWARGIDAN shugaban Najeriya Aisha Buhari, ta tofa albarkacin bakinta akan ce-ce-ku-ce da ke gudana a kasar sakamakon yin watsi da dokokin da ka iya ba mata damar samun kashi 35 cikin 100 na kujerun siyasa.ABUJA, NIGERIA — 

A wata takardar bayani da ta aiko da ita wa manema labarai ta yanar gizo, a ciki har da Muryar Amurka, Aisha Buhari ta bayyana bakin cikinta tare da nuna alhini akan abin da ta kira rashin adalci daga bangaren ‘yan Majalisar Dokokin kasar, to saidai kwararru a faninn siyasa na cewa abin da mata ke nema ba haka dimokradiya ta gada ba.

Shawarar da Majalisar Dokokin Najeriya ta zartas akan shaánin takarar mata a kundin tsarin mulkin da majalisar ta yi wa gyarar fuska, ta ci gaba da fuskantar Allah wadai daga masu ruwa da tsaki a Najeriya, a ciki har da Uwargidan Shugaban Kasa Hajiya Aisha Buhari.

Aisha Buhari
Aisha Buhari

A wata takardar bayani, Aisha ta ce ‘yan Majalisar Dokoki ba su yi amfani da dattako wajen fuskantar koke koken mata ba. Aisha ta ce matakin bai yi wa mata dadi ba, hasali ma, ganin yadda ita da matar Mataimakin Shugaban kasa, Dolapo Osinbajo suka nuna goyon bayansu ga dokar, ya kamata yan majalisa su dube su da idon rahama, su amince da wasu bangarorin dokar. Aisha ta ce za su sake zage damtse wajen tuntuba da yi wa dokar gyara yadda za ta samu karbuwa a zaurukan Majalisar nan gaba.

Ita ma tsohuwar Ministar Ma’aikatar Mata, Aisha Ismail ta bayyana raáyinta a game da wannan batun, inda ta ce za a hadu a dandalin zabe.

To saidai masanin harkokin siyasar kasa da kasa kuma malami a Jami’ar Abuja, Dokta Farouk Bibi Farouk ya yi nuni da cewa ba a taba yin dimokradiya da son zuciya ba.

Mata sun fito sun yi dafifi a kofar Majalisar inda suka nemi a sake duba dokokin a gyara su, domin matan Najeriya na fitowa kwansu da kwarkwatansu lokutan zabe suna kada kuri’a amma ba su cika samun manyan mukamai ba.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Siyasa

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Published

on

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Jam’iyyar APC reshen Jihar Zamfara ta dakatar da Ɗan Majalisar Wakilai, Aminu Jaji bisa wasu zarge-zargen da ake yi masa na cin amanar jam’iyyar.

Sakataren Yaɗa Labarai na Jam’iyyar APC na Jihar, Malam Yusuf Idris ne ya sanar da dakatarwar a wani taron manema labarai a Gusau a ranar Juma’a.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa, Jaji yana wakiltar mazaɓar Ƙaura-Namoda/Birnin-Magaji a Majalisar Wakilai a ƙarƙashin jam’iyyar APC.

Idris ya ce wasu zarge-zargen da ake yi wa Ɗan Majalisar sun haɗa da aikata rashin gaskiya da rashin zuwa tarurrukan jam’iyyar da kuma sauran ayyuka.

KU KUMA KARANTA: Kotun Najeriya ta bayar da umarnin dakatar da asusun banki fiye da dubu 1

Ya ce, matakin ya biyo bayan sanarwar dakatarwar da aka yi wa Jaji daga shugabannin jam’iyyar APC na mazaɓar Birnin-Magaji bisa zargin cin amanar jam’iyyar da dai sauran abubuwan da suka saɓa wa jam’iyyar.
Idris ya ce, “Kwamitin zartaswa na jam’iyyar APC na ƙaramar hukumar Birnin Magaji ne ya miƙa sanarwar dakatarwar zuwa hedikwatar jam’iyyar APC ta jihar.

Bayanai sun ce kwamitin zartaswar jam’iyyar APC na jihar ya gudanar da taron gaggawa a sakatariyar jam’iyyar da ke Gusau a ranar Juma’a 17 ga watan Mayu, 2024, inda aka gabatar da batun dakatar da Jaji ga ‘yan majalisar zartarwar jihar.

Continue Reading

Labarai

Tsohon gwamnan Katsina, Shema ya sauya sheƙa zuwa APC

Published

on

Tsohon gwamnan jihar Katsina, Ibrahim Shema, a hukumance ya koma jam’iyyar APC Mai mulki a jihar.

Shema, ya kasance gwamnan jihar a tsakanin shekarar 2007 zuwa 2015, a ƙarƙashin jam’iyyar PDP.

Tsohon gwamnan ya yi rajista ne a ofishin jam’iyyar na mazaɓar Shema, ƙaramar hukumar Dutsin-ma, inda shugaban jam’iyyar na jihar, Sani Aliyu-Daura ya ba shi katin zama ɗan jam’iyyar APC.

Lambar katin Shema ta zama ɗan jam’iyyar ita ce: 26551.

KU KUMA KARANTA:Gwamnatin Yobe za ta mayar da kwale-kwalen Dufuna mai shekaru 8,000 zuwa cibiyar yawon buɗe ido

Malam Aliyu-Daura ya yabawa Gwamna Dikko Raɗɗa da kuma tsohon gwamnan jihar Aminu Masari wanda ya gada, a bisa rawar da suka taka wajen ganin Shema ya sauya sheƙa.

Don haka ya tabbatar wa tsohon gwamnan cewa za a yi masa adalci kamar kowane ɗan jam’iyya.

Shugaban ma’aikata na Raɗɗa, Jabiru Abdullahi-Tasuri, shi ne ya miƙa katin zama ɗan jam’iyya ga Shema a madadin gwamnan a jiya Alhamis a Dutsin-ma.

Continue Reading

Labarai

Fusatattun matasa sun lakaɗawa kwamishina duka a wajen zaɓen fidda gwani

Published

on

Banji Ajaka, kwamishinan lafiya na jihar Ondo, ya gamu da fushin matasa a jiya Asabar yayin da ake gudanar da zaɓen fidda gwani na gwamna na jam’iyyar APC mai mulki a jihar.

Daily Trust ta gano cewa Dakta Ajaka, wanda ke Mazaɓar Ugbo 3, a ƙaramar hukumar, ana zarginsa da ɓoye takardar sakamakon zaɓen.

Shaidu sun tabbatar da faruwar lamarin a wata tattaunawa da suka yi da manema labarai, inda suka yi zargin cewa fusatattaun matasan ‘ya’yan jam’iyyar APC ne da ke adawa da tsarin da aka bi wajen gudanar da zaɓen.

Ɗaya daga cikin waɗanda suka shaida lamarin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana cewa rikicin ya faro ne lokacin da ‘yan ɗaya ɓangaren na jam’iyyar suka buƙaci ganin takardar sakamakon zaɓen na fidda gwani.

KU KUMA KARANTA:An yi jana’izar tsohon gwamnan Ondo, Rotimi Akeredolu

“Sun fusata ne suka buƙaci jami’in zaɓe ya ba su takardar sakamakon zaɓen sai kuwa ya ce ta na wajen Ajaka.

“Don haka suka yi masa duka a wurin, inda kuma garinsu ne. Jama’a sun fusata sosai da lamarin, inda rigimar ta ƙare a wajen.”

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Dakta Ajaka ya ce an zarge shi ne da riƙe takardar sakamakon zaɓen.

Ya yi bayanin cewa a lokacin da yake ƙoƙarin bayyana kansa, ’yan daban sun auka masa inda suka yi masa mugun duka.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like