No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga; Rabo Haladu.

WASU ‘Yan bindiga sun sace ɗaliban Kwalejin Kimiyyar Kiwon Lafiya mata huɗu a ranar Talata da daddare a Jihar Zamfara.

Wani mazaunin yankin ya faɗa cewa maharan sun afka wa gidan da ɗaliban ke zaune wanda ke wajen makarantar a garin Tsafe bayan sun tarar da jami’an tsaro na gadin kwalejin.

Shugagan kwalejin, Yusuf Idris Maradun, ya ce ɗalibai biyar ‘yan bindigar suka kama amma daga baya suka saki ɗaya daga cikinsu saboda ta kasa tafiya sakamakon lalurar ƙafa.

Rundunar ‘yan sanda a jihar ta ce jami’an tsaro sun duƙufa domin ganin an ceto ɗaliban da aka sace a gidan da suka kama haya suna kwana a cikin garin na Tsafe.

admin
adminhttps://neptuneprimehausa.com
Ni ɗan jarida ne mai zaman kansa. Mawallafi kuma mai sharhi a lamarin yau da kullum.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...