Connect with us

Labari

Ramadan 2022: Sheikh Dahiru Bauchi Ya Yi Bude Baki Tare Da Malaman Addinin Kirista A Kaduna

Published

on

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

TAWAGAR malaman addinin Kirista daga wasu sassa na Jihohin Arewacin Najeriya 19 a karkashin jagorancin Fasto yohanna buru sun ziyarci gidan Sheikh Dahiru Usman Bauchi dake Kaduna da nufin hada kai da sauran malaman addinin musulunci wajen yin buda baki na Azumin watan Ramadan, kana da neman kara karfafa alaka tsakanin kiristoci da musulmi.

Jagoran tawagar Fasto Yohanna Buru wanda yake Babban mai kula da Cocin Christ Evangelical and Life Intervention Ministry, dake Sabon Tasha, kaduna, sun yi buda bakin ne tare da takwarorinsu musulmai a gidan fitaccen malamin addinin musuluncin ne, Sheikh Dahiru Bauchi a yammacin ranar laraba a gidansa dake garin Kaduna domin kara kyautata alakar dake tsakaninsu.

Yayin da yake jaddada alakarsu wacce ta ke tun shekaru 11 da suka gabata, sun gudanar da yakin neman zaman lafiya a lokacin buda baki domin cudanya da mu’amala da galibin malaman addinin Musulunci na Najeriya, wadanda suka hada da Sarkin Musulmi, Alhaji Abubakar Sa’ad , Sheikh Ibrahim Yakub elzazzaky, Sheikh Dahiru Bauchi, Sheikh Salihu Mai Barota, Sheikh Mohammed ibn Abdul na Jihar Neja, da ma wasu kasashe makwabta na Afirka kamar Jamhuriyar Nijar da Jamhuriyar Benin, da nufin wa’azi da inganta zaman lafiya da hadin kai a lokacin buda baki.

Buru, ya yi nuni da cewa, zuwa yin buda bakin na watan Ramadana na ba da wata dama ga Kiristoci wajen yin cudanya da Musulmi da inganta fahimtar juna a tsakanin mabiya addinan biyu.

Jagoran tawagar kiristocin ya ce taron wanda shi ne karo na 11 kuma an yi shi ne domin inganta dangantakar addinai, tattaunawa, zaman lafiya, hadin kai, yafiya da kuma hakuri da juna tsakanin mabiya addinan Najeriya biyu.

“Muna yin haka ne domin inganta hadin kai a tsakanin addinai da kuma gujewa duk wani nau’in rikicin addini, siyasa da na kabilanci da ke haifar da zaman lafiya a yankin.”

“Mun shafe shekaru da dama muna tafe tare da limaman cocinmu da masu yin bishara da kuma dattawan coci don ganawa da manyan malaman addinin Musulunci domin yin bude bakin azumin watan Ramadanan da neman kara sanar da zaman lafiya da hadin kai a tsakanin al’umma baki daya.”

A bana Ramadan ya zo ne a cikin tsadar kayan abinci a kasuwanni, kalubalen rashin tsaro da tashe-tashen hankula sakamakon ta’addanci, ‘yan fashi da garkuwa da mutane a yankin, don haka a hada karfi da karfe wajen yin kira ga ‘yan Najeriya da su tashi tsaye wajen addu’ar Allah ya kawo mana dauki da kawo mana karshen rashin zaman lafiya da ya shafi dukkan kasashe.

“Dole ne mu tuna cewa mu iyali ɗaya ne a ƙarƙashin Allah. Dukkanmu muna da littattafai masu tsarki daga Allah ɗaya, mu ‘ya’yan Adamu ne da Hauwa’u, muna da abubuwa da yawa na kamanceceniya da juna.”

Da yake bayani bayan kammala shan ruwan, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya nuna farin cikinsa da ziyarar inda ya godewa mabiya addinin kirista daga Jihohin Arewa daban-daban da suke tabbatar da zaman lafiya da hadin kai a kasar.

Ya kuma jaddada bukatar a kara yin addu’a a kasa domin Najeriya ta shawo kan lamarin da ake ciki.

Yayin da yake kira ga shugabanni da su tuna da ranar shari’a, ya bukaci Musulmi da Kirista da su zauna lafiya da juna a kodayaushe.

Sheikh Dahiru Bauchi ya ce, “amininmu tsohon ministan wasanni Barista Solomon dallung bai samu damar halartar taron na bana ba, amma ya aika da sakon fatan alheri ga daukacin musulmin kasar nan na watan Ramadan 2022.

Ni ɗan jarida ne mai zaman kansa. Mawallafi kuma mai sharhi a lamarin yau da kullum.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like