Connect with us

Kasashen Waje

Yaƙin Ukraine: Janar-Janar Na Rasha Da Aka Kashe A Ukraine Zuwa Yanzu

Published

on

Daga Wakilinmu

MA’AIKATAR tsaron Ukraine ta ce an kara kashe wani janar na Rasha mai suna Yakov Rezantsev, a wani harin sama a kudancin birnin Kharson.

Rezantsev kwamandan runduna ta 49 ne ta sojojin Rasha.

Jami’an kasashen yamma sun ce shi ne janar na bakwai da ya mutu a Ukraine, kuma na biyu da aka kashe da ke rike da mukamin lafta janar mafi girma.

Ana zaton cewe karancin biyayyar dakarun sojin Rasha ne ya ke tilastawa manyan jami’ai zuwa fagen daga.

Cikin wata tattaunawa da aka yi har da dakarun Ukraine, wani sojan Rasha ya yi koken cewa Rezantsev ya yi ikrarin dole yakin ya kare a cikin sa’o’i, kwana huku kacal bayan fara yakin.

Kafafen sada zumunta na Ukraine a ranar Juma’a sun ce an kashe janar din ne a kusa da Kherson, wani wajen da Rasha ke amfani da shi a matsayin sansanin soji da Ukraine ta kai wa hari sau da dama.

An kara rawaito cewa an kashe wani laftana janar Andrei Mordvichev, a wani harin Ukraine a dao sansanin.

Kherson ne birnin Ukraine na farko da Rasha ta fara mamayewa, duk da cewa akwairahotanni da ke cewa akan samun zanga-zanga a kullum ta nuna kin jinin mamayar Rasha.

Duk da cewa Rasha ta tabbatar da mutuwar janar daya ne kawai, kyiv da jami’an yamma sun yi amannar sun kai bakwai janar din da aka kashe tun daga fara yakin.

Ka zalika an musanta mutuwar Manjo Janar Magomed Tushayev na tawagar kasa ta Chechen.

Ba abu ba ne da aka saba gani irin wadannan manyan jami’an na rasha su fita fagen daga, kuma kasashen yamma sun yi amannar cewa yanayin rashin biyayyar sojojin Rasha ne ya tilasta musu fita.

Turjiyar da dakarun Ukraine suka yi, da kuma kayanki marasa inganci da Rasha ke fama da shi, na daga cikin abubuwan da suka janyo mutuwar mutanen.

Dakarun Rasha sun dogara ne kan yadda harkokin sadarwa ke gudana a bude, misali ta wayar salula da tattaunawar da ake ta wayar jami’ai wadannan na basu damar sanin inda manyan jami’ai suke.

Rasha tace sojojinta 1,351 sun mutu tun daga fara yakin Ukraine, sai dai kasashen yamma sun ce adadin ya wuce haka.

Yakov Rezantsev

Rahotanni sun ce Laftana Janar Yakov Rezantsev an kashe shi ne a wani harin sama da aka kai kusa da garin Kherson.

An masa karin girma ne zuwa lafatana janar a bara, kuma shi ne kwamandan runduna ta 49 da ke lardin kudancin Rasha.

An ce yana cikin wadanda suka halarci yakin Syria.

Andrei Mordvichev

Jami’an Ukraine sun ce an kashe Andrei Mordvichev shi ma a Kherson a wani harin sama.

Shi ne kwamandan runduna ta 8 ta sojojin Rasha da ke yakin kudanci.

An ce an kashe shi ne a ranar 18 ga watan Maris.

Oleg Mityaev graphic

An ruwaito cewa an kashe Manjo Janar Oleg Mityaev a wani wuri kusa da birnin Mariupol, garin da ke kudu maso gabashin Ukraine inda aka ci gaba da kai manyan hare-hare a baya.

Wata tawaga a Ukraine ta yi ikrarin kashe shi.

Shi ne kwamandan tawagar sojin Rasha ta 150 da ke lura da makaman da ke tafiyar da su a motoci, wani sansani da aka bude a 2016, dake a lardin Rostov da ke kusa da iyakar Ukraine.

Ukraine ta yi ikirarin an kafa wannan tawaga ne domin ta shiga yakin da ake yi cikin sauki su mamaye yankin gabashin Ukraine, sai dai Rasha ta musanta hakan.

Andrei Kolesnikov graphic

Manjo Janar Andrei Kolesnikov, na cikin rundunar ta 29, an kashe shi ranar 11 ga watan Maris, kamar yadda majiyoyin Ukraine suka bayyyana.

Ba a fadi ko ta yaya aka kashe shi ba.

Bayan Kolesnikov ya kasance janar din Rasha na uku da aka kashe, daya daga cikin manyan jami’an yamma ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na PA cewa Rasha za su fuskanci matsalar rashin hadin kai daaga kananan dakarunsu tsakaninsu da manya.

Vitaly Gerasimov

Manjo Janar Vitaly Gerasimov, babban jami’i a runduna ta 41 an kashe shi a ranar 7 ga watan Maris a wajen birnin Kharkiv, kamar yadda ma’aikatar tsaro ta Ukraine ta bayyana.

Birnin Kharkiv da ke kusa da iyaka Rasha ya fuskanci muggan hare-haren dakarun Rasha.

Vitaly Gerasimov na cikin yakin Chechen na biyu, dakarun Rasha da suka yi yaki a Syria da kuma mamayar da Rasha ta yi wa Crimea a 2014.

Andrey Sukhovetsky

Sai Manjo Janar Andrey Sukhovetsky, mataimakin kwamandan rundunar da Gerasimov ya fito ne, an ce an kashe shi a ranar 3 ga watan Maris.

Kamar dai Gerasimov, shi ma Sukhovetsky na cikin tawagar da suka yi aiki a Crimea da Syria.

Ba kamar sauran janar din ba, mutuwar Sukhovetsky an sanar da ita a kafafen sada zumunta na Rasha kuma shi ma shugaban Vladimir Putin ya tabbatar da ita a wasu taruka.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Kasashen Waje

Trump da Harris sun yi tir da zanga-zangar ƙin jinin Isra’ila

Published

on

Trump da Harris sun yi tir da zanga-zangar ƙin jinin Isra'ila

Trump da Harris sun yi tir da zanga-zangar ƙin jinin Isra’ila

Zanga-zangar na zuwa ne a daidai lokacin da Firai ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ke ƙare yaƙin da ƙasar ke yi a Gaza, a yayin jawabi da ya yi a zauren Majalisar dokokin Amurka.

Manyan ‘yan takarar shugabancin Amurka biyu, mataimakiyar shugaban ƙasa Kamala Harris da tsohon shugaban ƙasa Donald Trump, sun ya yi Allah-wadai da zanga-zangar nuna adawa da Isra’ila wacce aka fara ranar Laraba a kusa da ginin majalisar dokokin Amurka.

Zanga-zangar na zuwa ne a daidai lokacin da Firai ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ke kare yaƙin da ƙasar ke yi a Gaza, a yayin jawabi da ya yi a zauren Majalisar dokokin Amurka.

Harris, wacce ta yiwu ita ce ‘yar takarar shugaban ƙasa ta jam’iyyar Democrat a zaɓen shekarar nan ta 2024, a cikin wata Sanarwa ta ce “Mun ga ayyukan Allah-wadai daga marasa kishin ƙasa masu zanga-zanga da munanan kalaman ƙiyayya a tashar jirgin ƙasa ta Union Station da ke kusa da ginin majalisar dokoki.”

KU KUMA KARANTA:Joe Biden ya janye daga takarar shugaban Amurka

A gaban tashar, masu zanga-zangar sun cire tutocin Amurka suka sanya Tutocin Falasɗinawa, sannan wani mutum ya yi amfani da jan fenti ya rubuta “Hamas na nan tafe” da manyan harrufa a kan wani babban sassaƙe. Bayan haka Masu zanga-zangar sun ƙona wani mutum-mutumi na Netanyahu da tutar Amurka.

Shi ma Trump, ya rubuta a shafin sa na sada zumunta na Truth cewa “Idan da waɗanda suka ta da tarzoma jiya a Washington ‘yan Republican ne, da yanzu dukkansu na tsare a gidan yari, suna fuskantar hukuncin ɗauri na shekaru 10 zuwa 20. Amma a ƙarƙashin wannan Gwamnatin, babu abin da zai same su.”

A jiya Alhamis Shugaban Amurka Joe Biden ya karɓi baƙuncin Firai Minista Benjamin Netanyahu a fadar White House, don tattaunawa da nufin ganin an cimma yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza da kuma sakin sauran mutanen da Hamas ta yi garkuwa da su, tun bayan harin da ta kai kan Isra’ila ranar 7 ga watan Oktoban bara.

Shugabannin biyu sun gana a Ofishin shugaban kasa, kwana daya bayan da dukkansu sun gabatar da muhimman jawabai. A ranar Laraba Netanyahu ya yi magana a gaban Majalisar Dokokin Amurka, inda ya kare yaƙin da ƙasarsa ke yi da mayaƙan Hamas.

Shi kuwa shugaba Biden ya yi jawabi game da dalilin da ya sa ya yanke shawarar janyewa daga takarar shugaban ƙasa a ranar Lahadin da ta gabata, tare da bayyana goyon bayansa ga mataimakiyarsa.

 

Dukkan shugabannin biyu sun gabatar muhimman jawabai a taƙaice kafin ganawar da suka yi ta sirri.

To sai dai gabanin ganawar, wani babban jami’in gwamnatin ƙasar ya shaidawa manema labarai cewa shugabannin biyun suna aiki kan cikakkun bayanai game da yarjejeniyar tsagaita wuta da kuma sakin waɗanda aka yi garkuwa da su, “wadda suka ce sun yi imani ana a matakin ƙarshe.”

Continue Reading

Kasashen Waje

An ceto wani jariri da aka kashe mahaifiyarsa a wani mummunan farmaki ta sama a Gaza

Published

on

An ceto wani jariri da aka kashe mahaifiyarsa a wani mummunan farmaki ta sama a Gaza

An ceto wani jariri da aka kashe mahaifiyarsa a wani mummunan farmaki ta sama a Gaza

An kashe aƙalla mutane 13 a wasu hare-hare uku da Isra’ila ta kai kan sansanonin ‘yan gudun hijira da ke tsakiyar Gaza cikin daren Juma’a zuwa jiya Asabar, a cewar jami’an kiwon lafiyar Falasɗinu, yayin da ake ganin ana samun ci gaba a tattaunawar tsagaita buɗe wuta a birnin Alkahira.

Daga cikin waɗanda suka mutu a sansanin ‘yan gudun hijiran Nuseirat da kuma sansanin ‘yan gudun hijiran Bureij, akwai yara uku da mace guda, a cewar ƙungiyoyin agajin gaggawa na Falasɗinawa da suka kai gawarwakin zuwa asibitin Al-Aqsa Martyrs da ke kusa. ‘Yan jaridan AP sun kirga gawarwakin mutane 13 a asibitin.

Mace macen baya-bayan nan na zuwa ne adaidai wani lokaci da ake bege gani a yakin da ya addabi Gaza, bayan da tawagar likitocin suka ceto jariri da rai daga wata mace Bafalasdina mai juna biyu da aka kashe a harin na jirgin sama da ya fada kan gidanta da ke Nuseirat da yammacin ranar Alhamis.

An kashe Ola al-Kurd mai tsohon ciki mai shekaru 25 tare da wasu mutane 6 a tashin bam ɗin, amma jami’an agajin gaggawa suka garzaya da su asibitin Al-Awda da ke arewacin Gaza da fatan ceto yaron da ke cikinta. Sa’o’i kaɗan bayan haka, likitoci sun shaida wa kamfanin dillancin labarai na Associated Press cewa an haifi yaron.

Jaririn da har yanzu ba a raɗa masa suna ba yana cikin koshin lafiya, sai dai yana fama da ƙarancin iskar oxygen kuma an sanya shi a cikin na’urar incubator, in ji Dr. Khalil Dajran. Mahaifin yaron ya samu rauni a wannan harin, amma ya tsira da ransa.

KU KUMA KARANTA:Isra’ila ta kashe Falasɗinawa 48 a Gaza a ƙasa da awa ɗaya

Yakin na Gaza, wanda ya ɓarke sanadiyar hari da Hamas ta kai wa kudancin Isra’ila a ranar 7 ga watan Oktoba, ya yi sanadin mutuwar mutane fiye da 38,900, a cewar ma’aikatar lafiyar yankin, wadda ba ta banbance tsakanin mayaka da fararen hula a kidayar ta.
Yakin ya haifar da bala’in jin kai a yankin Falasɗinawa da ke gabar teku, inda aka raba mafi yawan al’ummarta miliyan 2.3 da muhallansu tare da janyo yunwa mai yawa.

Harin na Hamas a watan Oktoba ya kashe mutane 1,200, galibi fararen hula, sannan mayaƙan sun yi garkuwa da kusan mutane 250.
Kimanin mutane 120 ne suka rage a hannu ake garkuwa da su, inda aka yi imanin kusan kashi uku daga cikinsu sun mutu, a cewar hukumomin Isra’ila.

Continue Reading

Kasashen Waje

Babban sakatare na jami’ar Gurguzu a Vietnam, Nguyen Phu Trong, ya rasu

Published

on

Babban sakatare na jami'ar Gurguzu a Vietnam, Nguyen Phu Trong, ya rasu

Babban sakatare na jami’ar Gurguzu a Vietnam, Nguyen Phu Trong, ya rasu

Nguyen Phu Trong, babban sakatare na jam’iyyar gurguzu mai mulki a Vietnam, kuma ɗan siyasa mafi ƙarfi a ƙasar, ya rasu sakamakon rashin lafiya na tsawon watanni, kamar yadda kafafen yaɗa labarai suka faɗa a ranar Juma’a.

KU KUMA KARANTA:Jam’iyar Republican ta tsayar da Donald Trump takarar shugaban ƙasa karo na uku
Ya rasu yana da shekaru 80 a duniya.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like