Connect with us

Gobara

Wata ma’adanar mai a Kano ta kama da wuta, an samu asarar rai da dukiya da gidaje

Published

on

Wata fashewa daga wata ma’adanar mai da ake zargin ba bisa ka’ida ba a Kano a ranar Litinin, 8 ga watan Janairu, ya kashe mutum ɗaya, ya ƙona aƙalla gidaje biyar da wata babbar mota.

Lamarin ya faru ne a unguwar Katango General dake Wailari, ta hanyar Western Bypass, daura da gidan Maryam Shekarau, dake kan titin Ring, Kano.

Kimanin sa’o’i uku aka kwashe tare da haɗin gwiwar jami’an hukumar kashe gobara ta jihar Kano da hukumar bada agajin gaggawa ta ƙasa NEMA da ma’aikatan kashe gobara daga gidan man Salbas wajen shawo kan gobarar.

Wani direban babbar motar da ake ƙira Aminu da ke cikin matatar man, ya ƙone ƙurmus ba a iya gane shi.

KU KUMA KARANTA: Gobara ta cinye ɗaruruwan shaguna a kasuwar Gwarzo

Jami’an hukumar kashe gobara sun gano gawar sa, yayin suka isa wurin da lamarin ya faru bayan isarsu Wajen.

“Gidaje biyar sun kona da ƙurmus sakamakon gobarar da ta girgiza mazauna unguwar,” in ji wani ganau.

An ceto wata tsohuwa da ta ƙasa tafiya daga ɗaya daga cikin gidajen. Haka kuma, an ceto wasu yara biyu daga wani gida, wanda mahaifiyarsu ta fita a guje ta bar su a ciki.

Ahmad Umar Gaya, ma’aikacin ofishin duba ababen hawa (VIO), ya shaida wa manema labarai cewa, yana bakin hanya ne ya ji ƙarar fashewar wani abu.

“Wurin, wanda ke tsakiyar gidajen zama a Katango a Wailari, ana amfani da shi ne wajen adana tarkacen manyan motoci da tireloli da kuma tace man injin da aka yi amfani da shi don wasu dalilai.

“Babu wanda zai iya bayyana ainihin abin da ya faru wanda ya kai ga fashewar. Tirelar da ke ɗauke da ganguna na man inji da ake yi amfani da su ta ƙone sakamakon gobarar, shima direban ya ƙone ƙurmus.

“A kusa da wurin akwai gidaje da mata da yara, kuma kusan gidaje biyar ne gobara ta ƙone.”

Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Boko Haram

An tabbatar da mutuwar masu juna biyu a cikin harin da aka kai a Borno

Published

on

An tabbatar da mutuwar masu juna biyu a cikin harin da aka kai a Borno

An tabbatar da mutuwar masu juna biyu a cikin harin da aka kai a Borno

An kasha aƙalla mutane 18, yayin da wasu 30 suka jikkata bayan wasu jerin hare-haren da ake zargin wasu mata ‘yan ƙunar baƙin wake ne suka kai a jihar Borno a jiya Asabar, in ji shugaban hukumar bayar da agajin gaggawa ta yankin.

Borno dai na cikin shekaru 15 na hare-haren masu iƙirarin kishin Islama wanda ya yi sanadiyar mutuwar dubban mutane tare da raba wasu miliyoyi da humallan su.

Duk da cewa sojojin Najeriya sun rage ƙarfin mayaƙan, amma har yanzu suna kai munanan hare-hare kan fararen hula da kuma wuraren tsaro.

KU KUMA KARANTA:Gobara ta tashi a matatar man Ɗangote

Barkindo Saidu, shine babban Daraktan Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Borno, ya ce wasu da ake zargin ‘yan ƙunar baƙin wake ne suka kai hari daban-daban a wajen bikin aure da jana’iza da kuma asibiti, inda suka kashe mutane tare da jikkata wasu da dama a garin Gwoza.

Saidu ya ce an tabbatar da mutuwar mutum 18, adadin da ya haɗa da ƙananan yara da manya da ma mata masu juna biyu.

Sai dai babu wata ƙungiyar ko wani mutun da ya ɗauki alhakin kai wannan harin.

Boko Haram da ISWAP da ta ɓalle kanta, su ne ƙungiyoyin ‘yan bindiga da suka fi yawan gudanar da ayyukan su a jihar Borno, wani babban yanki na karkara mai girman gaske.

Continue Reading

Gobara

Tinubu ya jajantawa mutanen da gobarar kasuwar Karu ta shafa

Published

on

Tinubu ya jajantawa mutanen da gobarar kasuwar Karu ta shafa

Tinubu ya jajantawa mutanen da gobarar kasuwar Karu ta shafa

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya miƙa saƙon jajensa ga ‘yan kasuwar da shaguna da dukiyoyinsu suka ƙone a gobarar da ta tashi a kasuwar Karu a daren Alhamis.

Sanarwar da hadimin shugaban ƙasar akan harkokin yaɗa labarai, Ajuri Ngilale ya fitar a ranar Juma’a ta ce, shugaban ƙasar ya yi takaicin samun labarin gobarar da ta shafi wani sashe na kasuwar.

Da yammacin ranar Alhamis, gobara ta laƙume wani yanki na kasuwar, inda ta lalata ɗimbim dukiya da sauran kayayyaki masu daraja.

KU KUMA KARANTA:Gobara ta tashi a matatar man Ɗangote

Sanarwar ta ƙara da cewar, shugaban ƙasa na miƙa saƙon jajensa ga ilahirin ‘yan kasuwar da wannan mummunan al’amari ya shafa, sannan yana ba su tabbacin samun tallafi daga gwamnatinsa.

Shugaban ƙasar ya kuma yi ƙira da a riƙa taka tsantsan da ɗaukar matakan kariya, domin kare afkuwar gobara da sauran bala’o’i a nan gaba.

Continue Reading

Gobara

Gobara ta tashi a matatar man Ɗangote

Published

on

Gobara ta tashi a matatar man Ɗangote

Gobara ta tashi a matatar man Ɗangote

Gobara ta tashi da yammacin yau a wani sashe na matatar man Ɗangote da ke kusa da Lekki a Legas.

Jami’an agajin gaggawa sun ɗauki matakin shawo kan lamarin, kuma a cewar rahotannin farko, ba a samu raunuka ba.

Kawo yanzu dai ba a san musabbabin tashin gobarar ba, kuma ana ci gaba da gudanar da bincike don gano girman barnar da aka yi da kuma abin da ya haddasa faruwar lamarin.

Da take mayar da martani kan gobarar a cikin wata sanarwa da Ɗangote ya fitar, mai ɗauke da sa hannun Anthony Chiejina, ƙungiyar ta ce, “Mun yi gaggawar shawo kan wata ‘yar karamar gobara a masana’antar sarrafa iska (ETP), a yau Laraba 26 ga watan Yuni.

KU KUMA KARANTA: Gobara ta kashe jarirai shida a Indiya

“Babu wani dalili na tashin hankali yayin da matatar ta ke aiki kuma babu wani rauni da aka samu ko lahani ga dukkan ma’aikatanmu da ke bakin aiki.”

Matatar dangote wani katafaren aiki ne da ake ginawa wanda ake hasashen zai iya tace ganga 650,000 a kowace rana.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like