Connect with us

Labari

Uba Sani Ya Bada Tallafin Kayan Agaji Ga Al’ummar Giwa, Kaura Na Miliyoyin Naira

Published

on

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

SANATA Uba Sani mai wakiltar Shiyyar Kaduna ta tsakiya a Majalisar Dattawa, ya bayar da kayan agaji da tallafi ga al’ummar da rikicin ‘yan bindiga ya shafa a karamar hukumar Giwa da Kaura.

A wani sakon dake dauke da sa hannun Abubakar Rabi’u Abubakar, Shugaban mazabar Shiyya na Sanatan a ranar Alhamis din da ta gabata, ya bayyana cewa Dan takarar Gwamnan ta Jihar Kaduna karkashin Jam’iyyar APC, ya bayar da tallafin ne biyo bayan halin kuncin da al’ummar suka tsinci kansu a yankunan a yan kwanakin nan.

Ya kara da cewa, Sanatan ya jajantawa al’ummar da abin ya shafa a wadannan al’ummomi tare da addu’ar Allah ya ba su ikon jure radadin rashin wadanda suka rasa rayukansu.

Ya ce “Idan za a iya tunawa dai, Sanatan a zauren majalisar dattawan, ya bayar da shawarar matakin da zai bai wa jami’an soji damar gudanar da ayyuka ba tare da tangarda ba, wajen shafe masu aikata laifuka a yankunansu.”

“Sanatan ya bayyana matukar bakin cikinsa dangane da hare-haren da ake kaiwa ‘yan kasa da ba su ji ba ba su gani ba da asarar dukiyoyinsu.”

Acewar Sakon, Kayayyakin da Sanatan ya raba sun hada da; Galan na manja, Buhunan shinkafa, kwalayen taliyar Noodles, tabarmi, barguna, da sauran kayan abinci na gida.

Tawagar da ta ziyarci karamar hukumar Kaura ta samu jagorancin Injiniya Namadi Musa wanda tsohon darakta janar na kungiyar addinai ta jihar Kaduna ne, tsohon shugaban karamar hukumar kajuru Honarabul Cafra Caino, shugaban karamar hukumar Jaba Honarabul Ben Jock. Honarabul Banta Bala Bantex, Honarabul Donatus Adamu, Honarabul Joy Akut da Saratu Abdulazeez.

A karamar hukumar Giwa, tawagar ta samu jagorancin Honarabul Bashir Zubairu Birnin Gwari, tsohon kakakin majalisar dokokin jihar Kaduna tare da mataimakin shugaban karamar hukumar Kaduna ta Arewa Honarabul Nazir Sunusi, Injiniya Jamil Ahmad Muhammad, Honarabul Ibrahim Shehu Haske da Alhaji Ibrahim Musa yayin da tawagar ta samu kyakkyawar tarba daga shugaban karamar hukumar Giwa, Kungiyoyi, shugabannin al’umma da sauran Jami’an Jam’iyyar.

Hakazalika, a Karamar Hukumar Kaura, Tawagar ta samu tarbar Majalisar Gargajiya ta Kaura, Wakilin Shugaban Karamar Hukumar Kaura, Kungiyar Cigaban Kaura da Kauran IDP Forum.

A karshe, Shugaban Mazabar Shiyyar Abubakar Rabi’u Abubakar, ya bayyana cewa tawagar ta ziyarci sansanonin ‘yan gudun hijirar da aka tanadar domin raba kayayyakin da su tare da jajanta musu bisa wannan abin takaici.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like