Connect with us

Labari

Sai Da Muka Yi Tafiyar Kilomita 3 A Kasa – Ya’u Abdullahi

Published

on

Daga; MUSTAPHA IMRANA ABDULLAHI.

SHUGABAN Jam’iyyar APC a karamar hukumar Gada dake Jihar Sakkwato, arewacin tarayyar Najeriya Alhaji Ya’u Abdullahi, ya kasance daya daga cikin mutanen da suka tsallake Rijiya da baya lokacin harin da ‘yan Ta’adda suka kai wa Jirgin kasa da ya fito daga tashar Jirgin kasa ta Idu daga Abuja zuwa tashar Rigasa kaduna.

Da yake bayyana irin yadda lamarin ya faru kasancewarsa daya daga cikin mutanen da ke cikin Jirgin lokacin da lamarin ya faru a wani wuri idan an wuce kauyen da Alheri Kam yake kimanin mintuna 20 a kai ga tashar Jirgin kasa ta unguwar Rigasa Kaduna, sai kawai suka ji Jirgin da suke ciki ya fara tangal tangal zuwa can sai wani abu ya fashe nan take kuma suka fara jin harbe-harben Bindiga ta ko’ina, wato harbin kan mai uwa da wabi.

“Ina cikin taragon Jirgi mai lamba sha Bakwai nan da nan muka kwanta kasa a cikin taragon jirgin da muke ciki, bayan mun ji alamun abubuwa sun lafa, wato yan ta’addan sun ja da baya zuwa can bayan kimanin kamar awa biyu sai muka ji ana kwankwasa taragon da muke har muka gane cewa Sojoji ne sannan aka bude”.

Ya’u, ya ci gaba da cewa hakika “jami’an tsaron da suke tare da mu sun yi kokari domin sun mayar da wuta sai dai an fi karfinsu ne kawai, su ma sojojin da suka kawo mana dauki duk sun yi kokari kwarai domin sun yi aiki tare da nuna dabarun aiki wajen fito da jama’a daga ramin da suka fada sakamakon fargabar da suka shiga.

“Sojojin da suka kai dauki sun rika Goya jama’a ne a bayansu su na fitowa da su daga cikin rami wadansu kuma da ke da sauran karfinsu sun rika kamo gabar duwatsun da ke wurin suna yin tafiya kamar su na kan tsani domin su fito, sai kuma sojojin suka sanya mu a layi muka zazzauna bayan duk mun shiga layin sai suka tayar da mu tsaye muka shiga layi suka yi amfani da hasken wata mota kirar hilux, suka yi amfani da fitilar motar sai su ce wa jama’a ku tafi ga motarku can idan an kusa zuwa gare ta sai a kara gaba da ita motar a haka har sai da muka yi tafiyar a kalla kilomita uku a kasa, sannan muka Isa bakin kwalta inda aka ajiye motocin da za su dauke mu, an jera su a gefen titi haka aka dauko mu aka ajiye mu a dai- dai bakin kasuwa wajen labentis, isowa wurin sai muka tarar ya zama wata kasuwa ne duk da Dare ya yi, amma mutane na nan su na jiran mu iso wurin”.

“Kai akwai wata mata da take tare da wani mutum bayan an sanya mu cikin layi muna tafiya, ita ba ta iya tafiya sai wani soja a Karbe kayan da take rike da su a doka a bisa kanshi ya ce wa mutumin da suke tare ya rike mata hannu, ana nan muka yi ta tafiya har zuwa wurin motocin da aka ajiye za su dauko mu, kuma ni ne a sahun farko da muka shigo cikin jerin dogayen motocin da suka dauko mu”. Inji Ya’u Abdullahi.

“To Alhamdulillah, ni Allah ya tseratar da ni gani cikin koshin lafiya sai hamdala ta Allah kawai, amma ban ta ba shiga cikin tashin hankali irin wanda na shiga ba a wannan halin.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like