Taron Bita: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci ‘Yan Najeriya Da Su Yi Rajistar Inshorar Takaful

0
370

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

WASU malaman ilimi da kwararru a harkar inshora sun buƙaci ‘yan Najeriya da suka hada da ‘yan kasuwa da su yi la’akari da rungumar inshorar Takaful. Sun bayyana cewa Inshorar ya kasance mafi inganci kuma mai ɗabi’a wanda ke da fa’idodi masu yawa ga duk al’umma ba tare da la’akari da addini, ƙabila, ko matsayin zamantakewa ba.

Bayanin hakan ya fito ne a taron Takaful da kamfanin Noor Takaful Insurance Limited ta shirya a ranar Laraba, 16 ga Maris, 2022, a Jihar Kano.

Da yake gabatar da jawabinsa na maraba, Shugaban Kamfanin Noor Takaful Insurance Limited, Mista Muhtar Bakare, ya bayyana cewa taron bitar na daya daga cikin dimbin hanyoyin da kamfanin ke da niyyar jawo hankalin al’umma da kuma wayar da kan jama’a da ake bukata game da inshorar Takaful.

Ya ce “Wannan shi ne karo na farko a jerin tarurrukan da Noor Takaful ke shirin gudanarwa a garuruwa daban-daban na kasar nan, kuma ya kamata mu fara wannan tafiya a Kano. Na yi farin cikin ambaton cewa an haifi Noor Takaful a Kano a shekarar 2015.

“Wannan taron na nufin ya ba mu damar jin ta bakin malaman addinin Musulunci da na ilimi ta yadda za a san Takaful za ta taimaka wajen tallafa wa kasuwanci da al’umma kamar yadda duniya ta ke mai saurin canzawa, da kuma kalubale.

Acewar Bakare, baje kolin nasu zai ci gaba da hulda da mutane a wurare daban-daban nan da kwanaki masu zuwa.

Shi ma da yake nasa jawabin, mataimakin shugaban kamfanin, Malam Aminu Tukur, ya bayyana cewa kamfanin ya yi matukar farin cikin sake dawo da inshorar Takaful a kasuwar Kano, bayan da ya fara tafiya daga tsohon birnin.

Tukur ya ci gaba da cewa, kamfanin ya jajirce wajen inganta hada-hadar kudi ta hanyar inshorar Takaful ta hanyar samar da kayayyakin da suka dace da kowane fanni na zamantakewa.

Yayin da yake bayani kan manufofin inshorar Takaful, ya jaddada cewa tana gudanar da ayyukanta ne ta hanyar hada kudade tare domin ‘yan uwantaka.

Da yake tsokaci a wajen taron, malamin addinin Islama Dakta Bashir Umar ya bayyana cewa abin farin ciki ne ganin yadda Kamfanin ke daukar kalubalen bunkasa Takaful. Hakan ya nuna aniyar inganta inshorar da’a a Najeriya.

A cewar Umar, yanzu babu wata hujja ga musulmi musamman na yin rajistar kayayyakin inshora na yau da kullum tunda akwai kayayyakin da a yanzu suka dace da Sharia.

Shi ma da yake nasa jawabin mataimakin daraktan cibiyar bankin musulunci na kasa da kasa na Jami’ar Bayero ta Kano Dakta Warshu Rabi’u ya bayyana cewa duk da cewa inshorar Takaful tana nan daram idan aka kwatanta da inshorar da aka saba yi, masana’antar ta samu gagarumin ci gaba a kasuwannin duniya har girman ta kai Dala $22m cikin kankanin lokaci.

Rabiu ya bayyana cewa da shirin baje kolin da Noor Takaful ta fara, tana da kwarin gwiwar cewa Najeriya za ta zama jigo a masana’antar nan gaba kadan.
Ya bayyana cewa akwai bukatar ‘yan Najeriya su yi amfani da ita ganin cewa tana aiki ne bisa ka’idojin Shari’a da ke jaddada darajar taimakon juna da ‘yan uwantaka.

“Dole ne in yaba wa Noor Takaful da ta fara wannan wayar da kan Jama’a domin hakan yana taimakawa wajen sanya Najeriya cikin taswirar duniya idan ana maganar inshorar shari’a.

Ya ce biyan rarar kudi da gaggawar biyan kudaden da’awar ita ce hanya mafi girma ta shiga kasuwa”, in ji shi.

A nata jawabin, Daraktar Cibiyar Bankin Musulunci da Kudi (IIBF) ta Jami’ar Bayero ta Kano, Farfesa Binta Jibril ta bayyana cewa, babu lokacin da ya fi dacewa da za a ilimantar da ‘yan Najeriya musamman na Arewacin kasar nan kan alfanun Inshora Takaful banda yanzu domin hakan zai taimaka wajen gyara kuskuren akidar cewa kowane nau’in inshora bai sabawa Musulunci ba.

Jibril ta ci gaba da cewa, a tsawon shekarun da suka gabata, al’ummar yankin Arewa na ci gaba da nuna shakku kan batun Inshora tun da ya saba wa tsarin addinin Musulunci.

“A baya, mutane sun yi ta shakku kan batun Inshora a kan cewa ba su san abin da za a yi amfani da kudadensu ba. Talakawan Arewa na damuwa ko za a yi amfani da jarinsa ko kuma kudadensa daidai da koyarwa Alkur’ani,” inji ta

Yayin da ta yaba wa mahukuntan kamfanin kan kawo irin wadannan damammaki a Arewa, ta bukaci maza da mata da su yi amfani da damar da suke da ita ta hanyar biyan duk wasu manufofin da ake da su.

Shi ma da yake jawabi, Manajan Daraktan Noor Takaful Insurance Limited, Rilwan Sunmonu, ya shawarci ‘yan Najeriya da su shiga cikin fa’idodin ta hanyar biyan kuɗi daban-daban.

Taron mai taken: “Takaful insurance in an increasingly unstable and the unsecurity world” ya samu halartar fitattun malamai a fannin ilimi da masana’antu, wasu daga cikinsu sun hada da wani malamin addinin Islama, Dakta Bashir Umar, tsohon kwamishina a NAICOM, Malam Mohammed Kari, Darakta. International Institute of Islamic Banking and Finance, (IIIBF), Bayero University Kano, Professor Binta Jibril da dai sauransu.

Kamfanin Noor Takaful Insurance Ltd, kamfanin inshorar Takaful, NAICOM ne ta kafa ta kuma ta ba ta lasisin da ya dace a watan Afrilun 2016 a matsayin cikakken kamfanin inshorar Takaful na farko a Najeriya mai kaso 100 na hannun jarin Najeriya.

Kamfanin a halin yanzu tana taka rawar farko da kuma jagoranci wajen buɗe yuwuwar inshorar Takaful ga Najeriya. NAICOM ne ke tsara tsarin aikinsa kuma tana ƙarƙashin Dokar Inshora ta 2003.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here