Connect with us

Siyasa

Shugabancin Najeriya 2023: PDP Za Ta Bude Kofar Takara Ga Kowa

Published

on

ALAMU sun nuna cewa babbar jam`iyyar hamayyar Najeriya wato PDP za ta bar kofa bude ga dukkan `ya`yanta da ke sha`awar takarar shugaban kasa daga kowane bangaren kasar su fafata.

Sai dai kokawar da masu neman takarar ke yi na neman raba kan `ya`yan jam`iyyar.

A halin da ake ciki lamarin ya raba jam`iyyar gida uku kuma siyasa na cewa kokawar za ta iya shafar makomar PDP a babban zabe mai zuwa.

Duk da cewa ba a san adadin masu neman takarar shugaban kasa a tutar jam`iyyar PDP ba, kasancewar jam`iyyar ba ta dakatar da sayar da fom ga masu bukata ba, sai dai take-taken fitattu a tsakanin wadanda suka riga suka bayyana aniyarsu ta neman takarar da su da magoya bayansu na neman raba jam`iyyar gida uku.

Rukunin farko ya kunshi gwamnan jihar Rivers da wasu gwamnoni da ke da ra`ayin lallai ludayi ya kewaya, wato sai mulki ya koma kudancin Najeriya.

Sai bangaren wasu masu neman takarar daga arewacin Najeriya, da ya hada da gwamnan jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal, da na Bauchi, Sanata Bala Muhammad, da kuma tsohon shugaban majalisar dattawa, Sanata Bukola Saraki, wato rukunin masu ra`ayin maslaha, wadanda ke bukatar su daidaita a bar takarar ga mutum guda.

Sai kuma bangare na uku, wanda wasu ke masa kirari da kai-kadai-gayya wato rukunin tsohon mataimakin shugaban Najeriya Atiku Abubakar da nasa magoya bayan.

Haka wadannan gidaje uku suke da irin nasu magoya bayan, ciki har da gwamnoni masu ci da tsofaffi da sauran jiga-jigan jam`iyyar PDP.

Skip Podcast and continue readingPodcastKorona: Ina Mafita?

Shiri na musamman da sashen Hausa na BBC zai dinga kawo muku kan cutar Coronavirus

Kashi-kashi

End of Podcast

Kowane bangare ya dukufa wajen neman takarar, har ma mafi yawansu na safa-da-marwar kai ziyara ga wasu tsoffin shugabnnin kasa da sauran masu karfin fada a ji a jam`iyyar.

Kuma ganin yadda idon kowane bangare ya rufe ne masana ke cewa abin da jam`iyyar PDP ke gudu ya faru. Dr Abubakar Kari, masanin siyasa ne a jami`ar Abuja, ya ce “Ita wannan rarrabuwar kai tana daukar kalar bangaranci ne, wannan abu ya ki ci ya ki cinye wa, yana da hadari kwarai da gaske ga jam’iyyar kuma idan ba ta yi hankali ba wanki hula zai kai ta dare”.

Sai dai duk da cewa jam`iyyar PDP na ci gaba amfani da salon jan-rai wajen fadar yankin da za ta bai wa takarar shugaban kasa, masana na cewa ko ba jima ko ba dade, ba ta da zabi sai ta tsallake siradin…kuma idan ta yi sake sai a yi mata sakiya.

Wannan ne ya sa Dr Abubakar Kari ke cewa sai ta yi taka-tsantsan.

“Muddin jam’iyyar PDP ta na so ta kai labari, to dole ne ta yi taka-tsantsan. Bangaren da za ta bari ya yi takara da kuma wanda zai yi mata takarar zai iya zama ‘yar manuniya ga irin tabukawa ko rashin tabukawa da za ta yi a zabukan 2023.

“Alal misali idan suka zabi dan wani bangare, to wanda ba wannan dan bangare ba, za su iya juya mata baya ko kuma su ci gaba da zama a ciki amma suna ungulu da kan zabo”.

Masanin ya kuma kara da cewa idan jam’iyyar PDP ta dauki dan takara wanda ba mashuhuri ba, to kamar sun bude hanya ne ga jam’iyyar APC ta ci zabe a shekarar 2023.

Sai dai wasu jiga-jigan jam`iyyar PDP ta saba da shiga irin wannan matsatsin tana fita.

Sanata Ibrahim Umaru Tsauri, tsohon sakataren jam`iyyar ne na kasa, kuma ya shaida wa BBC cewa “Jam’iyyar PDP ba ta tsoron rikicin cikin-gida, idan an kawo matsayi a shiyyarku a kan zoning to duk wanda ya cancanci yin takara na tsayawa, idan dan takarar ya wuce daya to abin da mukan yi shi ne sai mu ce a zo a zauna a yi abin da ake kira ‘consensus’ wato a fid da mutum guda idan ba zai yiwu ba sai a je a hau layi a yi zabe”.

Kwamitin da PDP ta kafa don yanke shawara a kan maganar yankin da za ta bai wa takarar shugaban kasa dai ya ce ya gama aikinsa, amma bai fadi gangariyar matsayinsa ba sai lokacin da zai danka wa kwamitin zartarwar jam`iyyar rahotonsa, duk kuwa da cewa wasu sun tsegunta wa manema labarai cewa jam`iyyar za ta bar takarar a bude ga kowa da kowa.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Siyasa

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Published

on

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Jam’iyyar APC reshen Jihar Zamfara ta dakatar da Ɗan Majalisar Wakilai, Aminu Jaji bisa wasu zarge-zargen da ake yi masa na cin amanar jam’iyyar.

Sakataren Yaɗa Labarai na Jam’iyyar APC na Jihar, Malam Yusuf Idris ne ya sanar da dakatarwar a wani taron manema labarai a Gusau a ranar Juma’a.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa, Jaji yana wakiltar mazaɓar Ƙaura-Namoda/Birnin-Magaji a Majalisar Wakilai a ƙarƙashin jam’iyyar APC.

Idris ya ce wasu zarge-zargen da ake yi wa Ɗan Majalisar sun haɗa da aikata rashin gaskiya da rashin zuwa tarurrukan jam’iyyar da kuma sauran ayyuka.

KU KUMA KARANTA: Kotun Najeriya ta bayar da umarnin dakatar da asusun banki fiye da dubu 1

Ya ce, matakin ya biyo bayan sanarwar dakatarwar da aka yi wa Jaji daga shugabannin jam’iyyar APC na mazaɓar Birnin-Magaji bisa zargin cin amanar jam’iyyar da dai sauran abubuwan da suka saɓa wa jam’iyyar.
Idris ya ce, “Kwamitin zartaswa na jam’iyyar APC na ƙaramar hukumar Birnin Magaji ne ya miƙa sanarwar dakatarwar zuwa hedikwatar jam’iyyar APC ta jihar.

Bayanai sun ce kwamitin zartaswar jam’iyyar APC na jihar ya gudanar da taron gaggawa a sakatariyar jam’iyyar da ke Gusau a ranar Juma’a 17 ga watan Mayu, 2024, inda aka gabatar da batun dakatar da Jaji ga ‘yan majalisar zartarwar jihar.

Continue Reading

Labarai

Tsohon gwamnan Katsina, Shema ya sauya sheƙa zuwa APC

Published

on

Tsohon gwamnan jihar Katsina, Ibrahim Shema, a hukumance ya koma jam’iyyar APC Mai mulki a jihar.

Shema, ya kasance gwamnan jihar a tsakanin shekarar 2007 zuwa 2015, a ƙarƙashin jam’iyyar PDP.

Tsohon gwamnan ya yi rajista ne a ofishin jam’iyyar na mazaɓar Shema, ƙaramar hukumar Dutsin-ma, inda shugaban jam’iyyar na jihar, Sani Aliyu-Daura ya ba shi katin zama ɗan jam’iyyar APC.

Lambar katin Shema ta zama ɗan jam’iyyar ita ce: 26551.

KU KUMA KARANTA:Gwamnatin Yobe za ta mayar da kwale-kwalen Dufuna mai shekaru 8,000 zuwa cibiyar yawon buɗe ido

Malam Aliyu-Daura ya yabawa Gwamna Dikko Raɗɗa da kuma tsohon gwamnan jihar Aminu Masari wanda ya gada, a bisa rawar da suka taka wajen ganin Shema ya sauya sheƙa.

Don haka ya tabbatar wa tsohon gwamnan cewa za a yi masa adalci kamar kowane ɗan jam’iyya.

Shugaban ma’aikata na Raɗɗa, Jabiru Abdullahi-Tasuri, shi ne ya miƙa katin zama ɗan jam’iyya ga Shema a madadin gwamnan a jiya Alhamis a Dutsin-ma.

Continue Reading

Labarai

Fusatattun matasa sun lakaɗawa kwamishina duka a wajen zaɓen fidda gwani

Published

on

Banji Ajaka, kwamishinan lafiya na jihar Ondo, ya gamu da fushin matasa a jiya Asabar yayin da ake gudanar da zaɓen fidda gwani na gwamna na jam’iyyar APC mai mulki a jihar.

Daily Trust ta gano cewa Dakta Ajaka, wanda ke Mazaɓar Ugbo 3, a ƙaramar hukumar, ana zarginsa da ɓoye takardar sakamakon zaɓen.

Shaidu sun tabbatar da faruwar lamarin a wata tattaunawa da suka yi da manema labarai, inda suka yi zargin cewa fusatattaun matasan ‘ya’yan jam’iyyar APC ne da ke adawa da tsarin da aka bi wajen gudanar da zaɓen.

Ɗaya daga cikin waɗanda suka shaida lamarin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana cewa rikicin ya faro ne lokacin da ‘yan ɗaya ɓangaren na jam’iyyar suka buƙaci ganin takardar sakamakon zaɓen na fidda gwani.

KU KUMA KARANTA:An yi jana’izar tsohon gwamnan Ondo, Rotimi Akeredolu

“Sun fusata ne suka buƙaci jami’in zaɓe ya ba su takardar sakamakon zaɓen sai kuwa ya ce ta na wajen Ajaka.

“Don haka suka yi masa duka a wurin, inda kuma garinsu ne. Jama’a sun fusata sosai da lamarin, inda rigimar ta ƙare a wajen.”

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Dakta Ajaka ya ce an zarge shi ne da riƙe takardar sakamakon zaɓen.

Ya yi bayanin cewa a lokacin da yake ƙoƙarin bayyana kansa, ’yan daban sun auka masa inda suka yi masa mugun duka.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like