Connect with us

Kungiyoyi

Shugaban NUJ Kaduna, Ta Yi Alkawarin Tallafa Wa Manufofin Aiwatar Da Tsarin Daidaiton Jinsi

Published

on

Daga; USMAN NASIDI Kaduna.

SHUGABAR kungiyar ‘yan Jaridu ta Najeriya (NUJ), reshen Jihar Kaduna, Asmau Yawo Halilu, ta bayar da tabbacin cewa kungiyar za ta bayar da gudunmawa dari bisa dari don ganin an yi nazari tare da cikakken aiwatar da daidaito tsakanin jinsi da zamantakewa na (GESI), a Jihar Kaduna.

Asmau, ta bada wannan tabbacin ne a lokacin da ta karbi tawagar kungiyar Women’s Connect Initiative da Gender Policy Unit na Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya da suka kai mata ziyarar neman goyon bayan sake duba manufofin KADGESI a jihar, wanda Rise Up da Public Health Institute suka tallafa mata.

A cewar shugaban kungiyar ta NUJ, galibin ‘yan jarida ba su da masaniya kan manufar KADGESI don haka akwai bukatar kungiyar ta sake dawowa cibiyar Kungiyar domin fadakar da ‘yan Jaridun kan wannan manufa.

“Kuma muna tabbatar muku a matsayinku na Kungiyar cewa da yardar Allah za mu taimaka muku ta hanyar zaburar da mambobinmu don bayar da rahoton shawarwarin da za su kai ga bitar, ba wai don ina nuna son zuciya a matsayina na mace ba, abu ne mai muhimmanci da ya shafe mu kai tsaye.

“Don haka da yardar Allah muna ba da tabbacin 100% na mambobinmu za su tashi tsaye kuma za su taka rawar gani a wannan fanni, ina ganin kafin karshen wannan rana, zan zabi mutum uku da za su shiga cikin tawagar ku.

“Idan a tarihin kungiyarmu a karon farko aka ba ni dama na zo na yi shugabanci, ka ga yana da muhimmanci, don haka me zai hana ku ba sauran matan su ma su ba da gudummawarsu. Ina addu’ar Allah Yasa wanda zai gajena ita ma ta zama mace don mu bar mazan su huta na ɗan lokaci don mu nuna iyawarmu.

“Da yawa daga cikinmu muna jin wannan manufar a karon farko, wasu kadan daga cikinmu sun saba da wannan manufa kuma ina ganin suma sun yi ta rubuce-rubuce a kan wannan manufar, shi ya sa suke yin hakan a nan tare da mu don ba da gudummawarsu.” Ta ce.

Asmau, ta gode wa kungiyar bisa amincewa da kungiyar ta NUJ a matsayin wani bangare na masu ruwa da tsaki da za su ingiza yin nazari tare da aiwatar da manufofin gaba daya.

Tun da farko, wani jami’in kungiyar Rise Up kuma mai gudanar da ayyuka na “Advocacy for Review of KADGESI Policy,” Victor Osae Ihidero, ya shaida wa mahalarta taron cewa bisa lura da kungiyar tasu, manufar KADGESI ba ta samun isasshiyar kulawar kafafen yada labarai, yana mai cewa ba za a iya cimma manufofin Kungiyar ba tare da tallafin kafofin watsa labarai ba.

“Ba za mu iya yin hakan ba tare da ‘yan jarida ba, ba za mu iya cimma burin da muka yi niyyar cimmawa ba tare da ‘yan jarida ba, shi ya sa muka zo nan muka kawo wannan takarda mu bayar da ita a hannun NUJ, domin ku bi ta ku gani ko akwai bangarori na manufofin da za su iya zama wani abu a ciki wanda za ku iya mayar da hankali a kai don rahoto.

“Ba za mu ci gaba da tafiya ba tare da Sakatariyar NUJ a wannan bita ba, domin idan har kafafen yada labarai ba su yi magana a kai ba a yanzu, bayan an gama nazari, gwamnati na iya duba lamarin ta ajiye a gefe idan ana maganar aiwatarwa.

“Amma inda aka samu matsin lamba daga kafafen yada labarai, kuma Gwamna mai zartaswa ya ga ‘yan jarida suna sha’awar hakan, hakan na iya kara masa sha’awar aiwatarwa akoda yaushe, ko mun so ko ba mu so, ina ganin shi ne ya fi kowa sanin jinsi. A Najeriya a halin yanzu gwamnatinsa tana rike da mukaman da aka nada mata kashi 48, abu ne da ya kamata a yi bikin Murnar.

“Kuma idan har ya bar wannan ofishin, ba mu san wanda zai zo ko zai kasance da alaka da jinsi ba, amma idan akwai wata manufa, muna da ka’ida, yana nufin cewa abin da ya samu a cikin lokaci zai iya yin tasiri a ci gaba da zama, wannan ne ya sa muka zo nan domin neman goyon bayan kafafen yada labarai domin bayar da rahotannin shawarwarin.”

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Kungiyoyi

Ƙungiyoyin musulunci sun raba wa marayu 900 abinci kyauta a Katsina (Hotuna)

Published

on

Daga Abbas Bamalli

A wani biki mai ƙayatarwa da aka gudanar a gidan marayu na Katsina, sama da marayu 900 ne suka sami farin ciki matuƙa a lokacin da suka samu liyafar cin abincin rana, wanda ƙungiyoyi masu zaman kansu na Musulunci na ƙasa da ƙasa suka yi shirya.

Amir Sultana daga ƙasar Turkiyya tare da haɗin gwiwar Munazzama Da’awa Al-Islam (MADA) daga ƙasar Sudan ne suka shirya taron tare da haɗin gwiwar ofishin uwargidan gwamnan jihar Katsina, Hajiya Zulaihat Raɗɗa.

Shugaban ƙungiyoyi masu zaman kansu, Mufti Ahmed, ya bayyana cewa kimanin marayu 700 a ƙaramar hukumar Katsina da 200 a Jibiya ne suka ci gajiyar wannan kyakkyawan shiri.

Ahmed ya jaddada cewa manufarsu ita ce sanya murmushi a fuskokin marasa galihu, musamman marayu, da ke nuna irin yadda ƙungiyoyin ke gudanar da ayyukan jin ƙai.

KU KUMA KARANTA: Zulum ya raba wa iyalai dubu 40 tallafin abinci da kuɗi a Konduga

An samo kuɗaɗe don shirin ne ta hanyar gudumawa daga mawadata da ɗaiɗaikun mutane da suka amince da ƙungiyoyi masu zaman kansu.

Mufti Ahmed ya bayyana cewa, “Ta hanyar tallafin mun gina rijiyoyin burtsatse kusan 36 a wurare daban-daban a jihar.”

Ya ci gaba da cewa, “Yana daga cikin shirinmu na yin amfani da ragowar kuɗaɗen wajen sanya murmushi a fuskokin marasa galihu, musamman marayu a cikin al’ummarmu.

Wani ɓangare na ayyukanmu shi ne rarraba Alƙur’ani mai girma da kuma bayar da tallafin kuɗi ga marasa galihu.” Baya ga cin abincin rana, ƙungiyoyin sun kuma bayar da gudummawar dalar Amurka 400 ga marayun, wanda hakan ya ƙara haɓaka tasirin ayyukansu na alheri.

Alhaji Isah Muhammad-Musa, kwamishinan ayyuka na musamman, ya yaba da wannan mataki na ƙungiyoyi masu zaman kansu, inda ya ce hakan ya ƙarawa ƙoƙarin Gwamna Dikko wajen tallafawa marasa galihu da marayu a jihar.

Ya bayyana cewa, uwargidan gwamnan ta shirya yin irin wannan aikin na jin ƙai nan ba da jimawa ba, tare da ƙara azama wajen ɗaukaka masu buƙata a cikin al’umma.

Kalli hotona a nan:

Continue Reading

Kungiyoyi

Za a yi taron ƙasashen Musulmai da na Larabawa a Saudiyya kan yaƙin Gaza

Published

on

Saudiyya ta ce za ta karɓi baƙunci taron ƙungiyar Haɗin Kan Ƙasashen Musulmai don tattauna yaƙin Gaza

Ministan zuba jari na ƙasar Saudiyya ya ce, nan da kwanaki masu zuwa ƙasar za ta karɓi baƙuncin taron koli na ƙasashen Larabawa da ƙasashen Musulmai domin tattaunawa kan yaƙin Isra’ila da Falasɗinu.

“Za mu gani a cikin ‘yan kwanaki masu zuwa, Saudiyya ta ƙira wani taron gaggawa na Larabawa a Riyadh,” in ji ministan zuba jari na Saudiyya Khalid Al-Falih, a taron Bloomberg New Economy Forum a Singapore.

KU KUMA KARANTA: An harba rokoki daga Gaza zuwa Tel Aviv

“A cikin kankanin lokaci, makasudin gabatar da waɗannan tarukan guda uku da sauran tarukan ƙarƙashin jagorancin Saudiyya shi ne a kai ga warware rikicin cikin lumana.”

Kamfanin dillancin labaran Etemad ya rawaito cewa, shugaban ƙasar Iran Ibrahim Raisi zai tafi Saudiyya a ranar Lahadi mai zuwa don halartar taron kolin Ƙungiyar Haɗin kan Ƙasashen Musulmai, wadda ita ce ziyarar farko da wani shugaban ƙasar Iran ya kai tun bayan Tehran da Riyadh suka kawo ƙarshen rashin jituwar da aka shafe tsawon shekaru ana yi ƙarƙashin wata yarjejeniya da China ta kulla a watan Maris.

Continue Reading

Jan hankali

Sun yi wa likita dukan kawo wuƙa saboda ‘yar uwarsu ta rasu a Asibiti

Published

on

A ranar Talata ne wani mutum da ɗansa suka fusata inda suka sauke fishin su akan wani babban likita da ma’aikaciyar jinya a cibiyar kiwon lafiya ta tarayya da ke Idi-Aba, Abeokuta bayan da ‘yar uwansu ya rasu a cibiyar.

Rikicin ya ɓarke ne da misalin ƙarfe 2:00 na safiyar ranar Talata, a sashen bayar da agajin gaggawa na asibitin jim kaɗan bayan wata mara lafiya mai shekaru 53 ta rasu.

Shugaban ƙungiyar likitocin Najeriya reshen jihar Ogun, Dakta Kunle Ashimi yayin da yake zantawa da manema labarai, ya yi Allah wadai da harin da ‘yan uwan mamaciyar suka kai wa biyu daga cikin ma’aikatan jinya,akan mutuwar matar a sakamakon ciwon zuciya.

KU KUMA KARANTA:Lauya ya yi wa tsohon mijin wacce yake karewa duka a kotu

Ashimi ya ce Dr Pelumi Somorin likitan ne wanda abin ya shafa,yayin da ba a tantance ko waye ma’aikaciyar jinya ba.

Ya bayyana cewa mahaifin da ɗan, sun mari likitan yayin da aka sanar da su mutuwar yar uwar su.

A cewar Ashimi, matar ‘yar shekara 53 da aka kawo asibitin da ciwon zuciya mai tsanani, wanda ita kanta bayan binciken da ta kawo daga cibiyar da aka turo ta, ya nuna cewa,ba za ta ɗauki fiye da kwana ɗaya ba, sai dai wani ikon Allah.

“Watau ta kasance a matakin ƙarshe na gazawar zuciyarta. An bayyana hakan ga ’yan uwan ta, lokacin da aka kawo ta wurin, amma duk da haka mun yi imanin cewa,Allah kan iya yin wani abu, kuma muna jin cewa ya kamata mu yi iya ƙoƙarinmu don ganin mun taimaka mata.

“Ya taɓa faruwa a baya cewa, wani mutum da ke cikin irin wannan yanayin ya samu sauki tare da kulawar da ta dace.

“Amma abin takaici, wannan majinyaciyar ta mutu da misalin karfe 2 na safe kuma mijin da ɗan marigayiyar suka faɗa kan likitan da ke kula da mara lafiyar lokacin da aka sanar da labarin rasuwarta.

“Sun mari likitan , daga baya kuma suka hau matar mutanen da ke kusa da su suka yi ta jibgarta.

“Waɗannan mutanen kuma sun ci mutuncin wata ma’aikaciyar jinya” in ji shi.

Shugaban ƙungiyar ya ce an sanar da ‘yan sanda game da lamarin, inda ya ƙara da cewa duk da kasancewar ‘yan sanda a wajen,ɗan ya ci gaba da cin mutuncin su.

“An kira ‘yan sanda kuma DPO na ofishin ‘yan sanda na Kempta ya jagoranci tawagar ‘yan sanda zuwa wurin.

“Duk da kasancewar ‘yan sanda, ɗan mamacin ,ya afkawa wata ma’aikaciyar jinya kuma duk ƙoƙarin kwantar da hankalinsa da aka yi, ya ci tura.

“A karshe an kai mutanen biyu zuwa ofishin ‘yan sanda na Kemta, inda aka ɗauki bayanansu da na likitan da aka kai wa harin, ma’aikacin jinya da kuma shaidun da ke kewaye.”

Shugaban na NMA, ya gargadi ‘yan Najeriya da su daina cin zarafin ma’aikatan kiwon lafiya, yana mai shan alwashin cewa, duk wanda aka samu da laifi za a gurfanar da shi a gaban kotu.

“Mun yanke shawarar cewa wannan zai zama na ƙarshe kuma ba za mu yadda a bamu haƙuri ba, mun yanke shawarar mika ƙarar zuwa kotu kuma gobe za mu kasance a kotu.

“An fara duk wata shari’a kuma za mu kai wannan ƙara kotu.

“Muna so mu yi kira da kuma gargaɗi ga duk waɗanda suke zuwa asibitoci a Ogun cewa ƙungiyar likitocin Najeriya, da sauran abokanta da kowane likita, ba za su amince da kalmar “ayi hakuri” nan ba daga yanzu, daga duk wanda ya zagi wani daga cikin membobinmu.

“Za mu yi iya bakin kokarinmu wajen gurfanar da irin waɗannan mutanen kuma ba za mu amince da rokon kowa ba komai girman mutum.

“Don haka, muna rokon duk wanda yake da hankali ya yi tunanin zai iya roƙon mu daga baya don faranta ran jama’a. Ba laifinmu bane”.

Ashimi ya jaddada cewa, cin zarafin ma’aikatan lafiya ya zama ruwan dare gama duniya, wanda har yanzu ba a warware shi ba duk da kamfen da aka yi na daƙile barazanar.

Ya ce “a duniya baki daya, wannan batu ne da ke ci gaba da gudana kuma an gudanar da yakin akan hana hakan, da dama a duk faɗin duniya na yakar tashe-tashen hankula da cin zarafi da ake yi wa ma’aikatan lafiya.

“Musamman a cibiyar kiwon lafiya ta tarayya a Abeokuta, jihar Ogun da sauran asibitocin da ke kewayen Jihar Ogun waɗanda ke ƙarkashin ikonmu a matsayin kungiyar likitocin Najeriya.

“Mun gudanar da yaƙi da hani,da irin halayyar nan, da dama a kan wannan taron a baya kuma bayan yawan rokon da muka yi, sai da muka roƙi likitocinmu da su karɓi uzurin waɗanda suke yin abun

“Abubuwa irin wannan ba sa raguwa, a zahiri, wannan yana faruwa sau da yawa a lokuta da dama.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like