Connect with us

Sakonni

SHEKARU 80: Al’umma Sun Yaba Da Irin Sadaukarwar Alhaji Bawa Garba (ABG)

Published

on

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

A RANAR 18 ga watan Fabrairu na shekarar 2022 Dattijo Alhaji Bawa Garba wanda aka fi sani da suna (ABG) ke cika shekaru 80 da haihuwa a duniya.

Wadannan shekaru na wannan Dattijo sun zama abin ci gaba da alfahari a gare shi duba da yadda ya sadaukar da rayuwar shi wajen gudanar da taimakon Jama’a ta fuskoki da dama ba tare da tsunduma kan shi cikin harkokin siyasa ba.

Sunan (ABG) ya yi tambari a kasar nan a matsayin wani tauraro mai haskawa wanda ya zama baya mai goya marayu wajen taimako da inganta rayuwar marasa ƙarfi.

Ga dukkanin wanda ya san (ABG) a tsawon shekarun da ya shafe yana ayyuka babu, shakka zai yi zaton Dattijon a yanzu ya haura wadannan shekaru na 80, wanda hakan ke nuna cewa wannan bawan Allah ya fara ayyukan taimakon al’umma tun yana matashi ɗan shekaru 20.

Tarihi ya nuna yadda Alhaji Bawa Garba (ABG) ya samar da makaranta ta yaƙi da jahilci ga jama’ar Arewa tun a shekarun 1967 zamanin yaƙin basasa inda ya ilmantar da ɗaruruwan jama’ar Arewa a wani yunkuri na kishin yankin da ganin an cike gurbin da ke da shi a tsakanin bangaren Kudu da Arewa.

A fili yake, Alhaji Bawa Garba (ABG) mutum ne mai fikira wanda ya tsara rayuwar shi wajen bunƙasa harkokin kasuwanci dake tafiya da zamani a Najeriya musamman a yankin arewacin kasar.

An haifi Alhaji Bawa Garba (ABG) a garin Garkiɗa dake yankin ƙaramar hukumar Gombi ta Jihar Adamawa, kuma ya fara nuna kwazo akan ayyukansa tun yana yaro karami a harkar noma da kiwo tare da mahaifinsa.

Bai yi ƙasa a gwiwa ba wajen shiga harkokin kasuwanci inda ya yi suna sosai a babbar kasuwar baje koli ta duniya wadda ta fara ci a shekarar 1979 a Kaduna.

Dattijo Alhaji Bawa Garba (ABG) ya kasance sahun farko na wadanda suka fara harkar samar da tauraron Ɗan Adam a Najeriya inda ya samar da Kamfanin tauraron Ɗan Adam a biranen Kaduna da Legas tare da ɗaukar dubban matasa aiki.

Tarihin cigaban birnin tarayya Abuja ba zai cika ba sai sai an ambato irin kwazo da Alhaji Bawa Garba ya yi musamman a shekarar 2006 lokacin da Nasiru El-Rufa’i yake matsayin Ministan Abuja, ta fuskar sufuri inda ya samar da motocin ɗaukar fasinja sama da 150 dake Jigilar babban birnin.

Akwai rayuwa abin koyi dangane da halayyar Dattijo Alhaji Bawa Garba (ABG) duba da irin kyakkyawar rayuwa da ya yi wajen taimakon jama’a, Hakazalika ɓangaren iyalinsa ya ba da kyakkyawar kulawa a gare su lamarin da a yau dukkanin ‘ya’yansa ke cikin rayuwa ingantacciya abin so ga kowa da kowa.

Matukar ana magana akan dattawa da Dattaku ya zama wajibi a sanya Alhaji Bawa Garba (ABG) a ciki matsayin abin koyi wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen ganin rayuwar al’umma ta cigaban matasa sun zama abin alfahari ga Jama’a.

Muna amfani da wannan dama wajen taya iyalan Alhaji Bawa Garba (ABG) murna da wadannan shekaru masu daraja da albarka, muna taya ‘yan uwa da iyalan Alhaji Bawa Garba ABG murna da wannan baiwa da Allah ya basu Allah ya karo masa wasu shekaru masu albarka da ƙarin lafiya Allahumma Amin.

Ni ɗan jarida ne mai zaman kansa. Mawallafi kuma mai sharhi a lamarin yau da kullum.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Al-Muhajir ya jadadda mahimmancin ilimin taurari a ziyararsa gidan jaridar Neptune Prime

Published

on

Fitaccen malamin addinin Musulunci, masanin taurarin gargajiya, kuma fitacce a kafafen sada zumunta na soshiyal midiya, Malam Sharif Al-Muhajiru ya kai ziyarar ban girma a ofishin Neptune Prime’s da ke Abuja ranar Litinin.

Malamin wanda ya samu tarba daga mawallafi kuma wanda ya kafa kamfanin, Dokta Hassan Gimba ya nuna jin daɗinsa kan tarɓar da ya samu daga Neptune Prime.

Da yake jawabi bayan gabatar da jawabin da shugaban ma’aikatansa Saminu Dauda ya yi, malamin ya jaddada muhimmancin likitancin Musulunci, ilmin taurari tare da nuna bakin cikinsa kan yadda fannin ke fuskantar rashin kulawa.

Malamin wanda kuma yake rike da sarautar gargajiya ta Majidadin Yakanaje ya kuma bayyana hanyoyin da zai bi wajen magance matsalar sihiri da aljanu da ke addabar al’ummar mu a yau.

KU KUMA KARANTA:Zamu cigaba da Addu’a ga Yobe da Najeriya don samun zaman Lafiya- Shugaban Izala

Ya ƙara da cewa akwai hanyoyin da za a bi wajen magance matsalar rashin tsaro da rashin shugabanci nagari ta fuskar ruhi.

A nasa ɓangaren, mawallafin jaridar Neptune Prime, Dokta Hassan Gimba ya bayyana jin daɗinsa da ziyarar tare da yin alkawarin duba yadda kamfanin zai yi aiki tare da malamin.

Yayin da yake jaddada mahimmancin ilimi, Dakta Gimba ya ce ya ji daɗin ganin matashi kamar Al-Muhajir da ke ƙoƙarin ƙulla alaƙa tsakanin ilimin taurari da na gargajiya da na zamani, da kuma magungunan ganye.

Continue Reading

Labarai

Buhari da Atiku sun aike da sakon Allah Ya kara lafiya ga Sheikh Ɗahiru Bauchi

Published

on

Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari a ranar Alhamis ɗin da ta gabata, ya yiwa Sheikh Dahiru Usman Bauchi fatan samun sauki daga rashin lafiya.

Shugaban, a sakon da ya aikewa jagoran Ɗarikar Tijjaniyya, wanda Ministan Sadarwa da Tattalin Arziki na zamani, Farfesa Isa Ibrahim Ali Pantami ya mika a madadinsa, ya ce yana yi wa Sheikh fatan samun lafiya cikin gaggawa.

Shugaba Buhari a cikin wata sanarwa da ya fitar ta hannun mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Malam Garba Shehu, ya yi addu’ar Allah ya kara wa jagoran addinin Musulunci lafiya domin ya ci gaba da jagorantar mabiyansa da al’ummar kasar nan, a ƙoƙarin gina al’umma mai cike adalci da tausayi.

“Addu’ata ta gare shi, Allah ya jara masa lafiya da samun lafiya cikin gaggawa,” inji shi.

KU KUMA KARANTA:Rashin tsaro: Rarara ya shirya addu’a ta musamman a Kano

Shaikh Ali Isa Pantami ya kai rahoto ga shugaban ƙasa cewa, halin da Sheikh din ke ciki yanzu da sauki, ya ƙara da cewa jagoran na addinin musuluncin ya godewa shugaban ƙasa bisa kulawar da ya nuna masa, tare da addu’ar Allah ya ci gaba da basu nasarar gudanar da mulki, a bangaren gina kasa, zaman lafiya, da ci gaba.

A nasa ɓangaren, ɗan takarar shugaban ƙasa na babbar jam’iyyar adawa ta PDP Alhaji Atiku Abubakar shima ya aiki da nasa saƙon nemawa shaikhin malamin sauƙi a shafinsa na tweeter.

Atiku Abubakar ya ce “Yanzun nan na sami labarin mai tada hankali cewa Sheikh Ɗahiru Bauchi shugaban Ɗarikar Tijjaniyya a Najeriya ba shi da lafiya.

“Bisa la’akari da irin kyakykyawan jagoranci da abokantaka da Shehin Malamin yake yi da jama’a a faɗin kasar nan, ina mika sakon fatan alheri da samun lafiya cikin gaggawa.

“Allah ya baka lafiya da gaggawa, Sheikh Dahiru Usman Bauchi da fatan Allah ya kare ka, ya kuma kara maka karfin gwiwa akan cigaba da yiwa al’ummar mu hidima” in ji Atiku Abubakar.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like