Connect with us

Siyasa

Sardaunan Badarawa Ya Raba Shinkafa Da Kudi Na Kusan Kimanin Naira Miliyan 45

Published

on

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

TSOHON Shugaban riko na Kaduna ta Arewa, Honarabul Usman Ibrahim wanda aka fi sani da Sardaunan Badarawa, ya raba buhuhunan shinkafa da kudi na kusan kimanin Naira Miliyan 45 ga wakilai na Jam’iyyar PDP a shiyyar Kaduna ta tsakiya.

Honarabul Ibrahim wanda shi ma dan takarar Sanata ne na shiyyar Kaduna ta tsakiya ya kuma bayar da wasu sabbin motoci uku a lokacin da yake bayyana ra’ayinsa na tsayawa takara a Kaduna.

Yayin da yake ba da tabbacin sanya muradin masu goyon bayan Jam’iyyar a gaba, dan takarar Sanatan ya bayyana cewa, idan wakilan suka zabe shi ya lashe Zaben fidda gwani, jam’iyyar PDP za ta samu gagarumin rinjaye wajen lashe Zaben gama gari domin a cewarsa farin jini da kwarjinin da ya bayyana cewa ya na da shi zai kasance wani abun da zai iya zama dalilin da zai sa a zabe shi don haka dole ne a yi la’akari da ‘yan takarar da ke neman mukaman Zaben.

Ya yi nuni da cewa tuni jam’iyyar adawa a jihar ta fara shirin korar jam’iyyar APC daga gidan gwamnatin Kaduna da duk wasu mukamai da za su yi takara.

Dan siyasar ya kara da cewa PDP za ta ci gaba da zama a gidansa, inda ya tuna yadda ya rasa gidansa dauke da motoci goma biyo bayan rikicin zaben 2011 a Kaduna da sauran Jihohin Arewa.

Sardaunan Badarawa wanda kuma ke rike da sarautar San-turakiin Hausa na gargajiya, ya lura cewa siyasa ta shafi yi wa jama’a hidima ne a matakin kasa wanda ya ce bukatunsu ya kamata su zama abin damuwa ga aikin duk wani zababben shugaba.

Mai ba da agajin ya ce ƙara darajar rayuwar jama’a shi ne ya mayar da hankali a kai bisa harkokin jama’a.

Acewarsa, ya kasance mai goyon bayan PDP tun bayan komawarsa jam’iyyar da ya bayyana a matsayin Jam’iyya mai Karfi wacce za ta yi nasara wanda hakan yasa yake son jam’iyyar adawa mai karfi da za ta iya kwace mulki daga hannun APC.

Hon. Ibrahim ya yi alkawarin cewa ba zai ba yankin Kaduna ta tsakiya kunya ba idan har aka ba shi wakilcin shiyyar Sanata a zaben 2023.

Wani daya daga cikin wakilen wanda ya bayyana kansa a matsayin Musa Lawal ya yabawa dan siyasar bisa karamcinsa da jajircewarsa ga jam’iyyar, inda ya sha alwashin tara sauran wakilai domin samun nasarar Sardaunan Badarawa a zaben fidda gwani da na kasa baki daya.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Siyasa

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Published

on

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Jam’iyyar APC reshen Jihar Zamfara ta dakatar da Ɗan Majalisar Wakilai, Aminu Jaji bisa wasu zarge-zargen da ake yi masa na cin amanar jam’iyyar.

Sakataren Yaɗa Labarai na Jam’iyyar APC na Jihar, Malam Yusuf Idris ne ya sanar da dakatarwar a wani taron manema labarai a Gusau a ranar Juma’a.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa, Jaji yana wakiltar mazaɓar Ƙaura-Namoda/Birnin-Magaji a Majalisar Wakilai a ƙarƙashin jam’iyyar APC.

Idris ya ce wasu zarge-zargen da ake yi wa Ɗan Majalisar sun haɗa da aikata rashin gaskiya da rashin zuwa tarurrukan jam’iyyar da kuma sauran ayyuka.

KU KUMA KARANTA: Kotun Najeriya ta bayar da umarnin dakatar da asusun banki fiye da dubu 1

Ya ce, matakin ya biyo bayan sanarwar dakatarwar da aka yi wa Jaji daga shugabannin jam’iyyar APC na mazaɓar Birnin-Magaji bisa zargin cin amanar jam’iyyar da dai sauran abubuwan da suka saɓa wa jam’iyyar.
Idris ya ce, “Kwamitin zartaswa na jam’iyyar APC na ƙaramar hukumar Birnin Magaji ne ya miƙa sanarwar dakatarwar zuwa hedikwatar jam’iyyar APC ta jihar.

Bayanai sun ce kwamitin zartaswar jam’iyyar APC na jihar ya gudanar da taron gaggawa a sakatariyar jam’iyyar da ke Gusau a ranar Juma’a 17 ga watan Mayu, 2024, inda aka gabatar da batun dakatar da Jaji ga ‘yan majalisar zartarwar jihar.

Continue Reading

Labarai

Tsohon gwamnan Katsina, Shema ya sauya sheƙa zuwa APC

Published

on

Tsohon gwamnan jihar Katsina, Ibrahim Shema, a hukumance ya koma jam’iyyar APC Mai mulki a jihar.

Shema, ya kasance gwamnan jihar a tsakanin shekarar 2007 zuwa 2015, a ƙarƙashin jam’iyyar PDP.

Tsohon gwamnan ya yi rajista ne a ofishin jam’iyyar na mazaɓar Shema, ƙaramar hukumar Dutsin-ma, inda shugaban jam’iyyar na jihar, Sani Aliyu-Daura ya ba shi katin zama ɗan jam’iyyar APC.

Lambar katin Shema ta zama ɗan jam’iyyar ita ce: 26551.

KU KUMA KARANTA:Gwamnatin Yobe za ta mayar da kwale-kwalen Dufuna mai shekaru 8,000 zuwa cibiyar yawon buɗe ido

Malam Aliyu-Daura ya yabawa Gwamna Dikko Raɗɗa da kuma tsohon gwamnan jihar Aminu Masari wanda ya gada, a bisa rawar da suka taka wajen ganin Shema ya sauya sheƙa.

Don haka ya tabbatar wa tsohon gwamnan cewa za a yi masa adalci kamar kowane ɗan jam’iyya.

Shugaban ma’aikata na Raɗɗa, Jabiru Abdullahi-Tasuri, shi ne ya miƙa katin zama ɗan jam’iyya ga Shema a madadin gwamnan a jiya Alhamis a Dutsin-ma.

Continue Reading

Labarai

Fusatattun matasa sun lakaɗawa kwamishina duka a wajen zaɓen fidda gwani

Published

on

Banji Ajaka, kwamishinan lafiya na jihar Ondo, ya gamu da fushin matasa a jiya Asabar yayin da ake gudanar da zaɓen fidda gwani na gwamna na jam’iyyar APC mai mulki a jihar.

Daily Trust ta gano cewa Dakta Ajaka, wanda ke Mazaɓar Ugbo 3, a ƙaramar hukumar, ana zarginsa da ɓoye takardar sakamakon zaɓen.

Shaidu sun tabbatar da faruwar lamarin a wata tattaunawa da suka yi da manema labarai, inda suka yi zargin cewa fusatattaun matasan ‘ya’yan jam’iyyar APC ne da ke adawa da tsarin da aka bi wajen gudanar da zaɓen.

Ɗaya daga cikin waɗanda suka shaida lamarin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana cewa rikicin ya faro ne lokacin da ‘yan ɗaya ɓangaren na jam’iyyar suka buƙaci ganin takardar sakamakon zaɓen na fidda gwani.

KU KUMA KARANTA:An yi jana’izar tsohon gwamnan Ondo, Rotimi Akeredolu

“Sun fusata ne suka buƙaci jami’in zaɓe ya ba su takardar sakamakon zaɓen sai kuwa ya ce ta na wajen Ajaka.

“Don haka suka yi masa duka a wurin, inda kuma garinsu ne. Jama’a sun fusata sosai da lamarin, inda rigimar ta ƙare a wajen.”

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Dakta Ajaka ya ce an zarge shi ne da riƙe takardar sakamakon zaɓen.

Ya yi bayanin cewa a lokacin da yake ƙoƙarin bayyana kansa, ’yan daban sun auka masa inda suka yi masa mugun duka.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like