Connect with us

Labari

SANARWA: Hasashen NIMET, NIHSA ya ja hankalin Jihar Yobe kan ambaliyar ruwa

Published

on

Hukumomin kula da yanayi a Nijeriya: ‘Nigeria Meteorological Agency (NIMET)’ da takwararta ta ‘Hydrological Services Agency (NIHSA)’ sunyi hasashen cewa jihar Yobe ta na ɗaya daga cikin jihohi 32 a ƙasar nan wayanda ake tsammanin za su fuskanci ambaliyar ruwa a kwanaki uku masu zuwa.

Hukumomin sun bayyana hakanne a cikin wani sakamakon yanayi da suka fitar ranar Talata.

Sunyi hasashen cewa za’ayi ruwan sama kamar da bakin ƙwarya wanda zai janyo ambaliya a jihohin a Yobe da jihohi kamar Sokoto, Zamfara, Katsina, Kaduna, Kano, Jigawa da Bauchi.

Sauran sun hada da Gombe, Kebbi, Neja, Babban Birnin Tarayya na Abuja, Plateau, Adamawa, Taraba, Kwara, Oyo, Lagos, Ondo, da Ogun. Haka abin zai kasance a Edo, Delta, Bayelsa, Cross River, Akwa Ibom, Benue, Inugu, Ebonyi, Imo, Anambra, Abia da Rivers.

Hukumomin sun ja hankali da cewa ambaliyar zai iya shafar gidajen al’umma, gonaki, hanyoyi da gadoji.

Bayan wannan hasashe da hukumomin suka yi, yana da muhimmanci jama’a su dauki ingantaccen mataki, musamman al’ummar jihar Yobe dangane da sakamakon da zai biyo bayan ambaliyar ruwan, wanda ya zo ta dalilin sauyin yanayin da aka samu a wannan shekara.

Wanda sakamakon hakan, jama’ar da suka fi fuskantar matsalar ambaliyar ruwan sune qananan hukumomin Potiskum, Gashua, Nguru, Fika, Gaidam, Damagum, Gujba, Gulani, Damaturu haxi da garuruwan da ke zaune kusa da hanyoyin ruwa, gwamnatin jihar Yobe tana shawartar su cewa su dauki ingantattun matakai a irin wannan lokaci na damina.

A ƙoƙarin ganin ta ci gaba da kare rayuka da dukiyar jama’ar jihar, ta hanyar amfani da matakai daban-daban, gwamnatin jihar Yobe ta dauki muhimman matakai da ingantattun tsare-tsare wajen bayar da daukin gaggawa: yunqurin daqile afkuwar ambaliyar, shirin ko-ta-kwana, kai daukin gaggawa tare da na aikin farfado da wuraren da ibtila’in ya rutsa dasu, ta hanyar Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar Yobe (SEMA) da takwararta ta NEMA.”

Hukumar SEMA kowane lokaci a shirye take wajen aiki babu dare ba rana a duk lokacin da wani ibtila’i ya faru a fadin jihar, domin kai daukin gaggawa, tallafa wa wayanda abin ya rutsa dasu da sake farfado da wuraren da al’amarin ya shafa.

Dadin daɗawa gwamnatin jihar Yobe za ta dauki matakin kafa kwamitocin bayar da agajin gaggawa a qananan hukumomin jihar (LGEMC) wayanda za su rinqa bayar da tallafin gaggawa a matakin farko ga jama’a, kafin zuwan Hukumar SEMA.

Bayan ingantattun matakan da gwamnatin jihar ke dauka domin magance matsalar ambaliyar ruwan, ana kira ga jama’a da cewa su nisanci al’adar zuba shara kan hanya ko a magudanun ruwa, musamman unguwannin da suke fuskantar barazanar ambaliyar ruwa, da bayar da kula ta musamman ga raunana; tsoffi, naqasassu da yara, a irin wannan lokaci.

Akwai buƙatar kwamitocin kula da tsabtace muhalli a qananan hukumomi har da qungiyoyin taimakon kai da kai, su fadakar da mambobin su wajen ci gaba a aikin tsabtace muhalli ta hanyar yashe magudanun ruwa da gyara hanyoyin ruwa da dakatar da jama’a yin gini kan hanyar ruwa.

Manoman mu, musamman fadama da wayanda gonakin su suke kusa da koguna, muna basu shawara su yi amfani da sauyin yanayin wajen samun zarafin shuka amfanin gonarsu zuwa girbi, ba tare da fuskantar wata barazana ga amfanin ko dabbobin su ba.

Yusuf Ali
Babban Mai Taimaka Wa Gwamna Mai Mala Buni a Fannin Yada Labaru na Zamani Tare Da Dabarun Sadarwa.

3 Comments

3 Comments

  1. Pingback: Ambaliyar ruwa ta haddasa asarar rayuka da lalata gidaje same da100 a Gombe | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: Anyi hasashen hazo da zazzafar ƙura na kwana 3 daga yau Alhamis | Neptune Prime Hausa

  3. Pingback: Jihohin Kogi, Anambara da Yobe za su fuskanci mummunar ambaliyar ruwa a daminar bana – NiMet | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like