Connect with us

Siyasa

Rikicin APC A Kano: ‘Yan Gandujiyya Sun Mayar Wa Su Shekarau Martani

Published

on

Daga Wakilinmu

Gwamna Ganduje da Sanata Shekarau

Ɓangaren  jam`iyyar APC da gwamna Kano ke jagoranta ya ce a shirye yake ya yi tafiya da ɓangaren Senata Ibrahim Shekarau ba tare da nuna wani bambanci ba.

Hakan ya biyo bayan matakin kotun daukaka kara a Abuja ta tabbatar wa bangaren Gandujen shugabancin jam’iyya, inda uwar jam`iyyar ba ta yi jinkiri ba wajen bai wa bangaren shaidar shugabanci a jihar Kano.

Bangaren Senata Shekarau dai ya nuna rashin jin dadinsa game da wannan matakin da kuma wadansu kalamai da suke ce gwamna Ganduje ya yi, wadanda suke zargin cewa babu dattako a ciki.

To amma Honarabul Kabiru Alhassan Rurum, dan majalisar wakilai kuma daya daga cikin jiga-jigan ɓangaren gwamna Ganduje ya shaidawa BBC cewa su fatansu shi ne ɓangaren Sanata Ibrahim Shekarau ya manta da komai su koma tamkar yadda suke a baya, wato a gudu tare a tsira tare.

”Dukkanin mu uwa daya uba daya muke, ‘ya’yan jam’iyya daya ne illa sabani da ya zo da rashin fahimta kuma wannan ba zai hana mu sake zama mu ci gaba da tattaunawa ba.

Fatana shi ne da mu da mu kai nasara da su da sukai akasin hakan mu hada kai kamar yadda muka hada kai 2019, domin ko babu komai jam’iyyar mu daya kuma dukkaninsu shugabannin mu ne.

Mu na ganin lallai lokaci ya yi da ya kamata mu hada kai, a yafi juna kuma a gudu tare a tsira tare,” in ji Rurum.

Ya ce ko da yake a baya an yi maganganun da ba su yi wa ɓangaren sanata Shekarau dadi ba, amma magana zarar bunu ce murna da shauki da annushuwa ne suka sanya gwamna Ganduje fadar maganar da ake zargin ya fada din.

Rurum ya kara da cewa, amma a bayyani na biyu lokacin da suka je karbar satifiket na shugaban jam’iyya, ya yi jawabin da kira a gare su da su yi hakuri, su zo ayi tafiyar nan tare.

Ya kuma ce gwamnan a shirye ya ke ya sake nemansu domin a ci gaba da tattaunawa don hada kai kamar yadda ake a baya.

Kan batun da bangaren Sanata Shekarau ke yi na ganin uwar jam’iyya ba ta yi adalci ba Rurum ya ce: ”mu masu biyayya ne da hukuncin kotu da uwar jam’iyya ko ya yi dadi ko bai yi ba, sanna ita jam’iyya ita ce ta san dalilin da ya sanya ta dauki wannan matakin dan haka hakkin ta ne ta yi bayanin dalilin da ya sa su daukar wannan hukuncin”.

Ɓangaren da Sanata Ibrahim Shekarau ke jagoranta na jam’iyyar APC a Kano ya ce za su tafi Kotun Koli don ci gaba da kalubalantar bangaren su Gwamna Ganduje a rikicin shugabancin jam’iyyar da su ke yi.

Tsohon gwamnan Kanon ya kuma nuna rashin jin dadinsa da wasu kalmomin batanci da ya ce gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya yi amfani da su jim kadan bayan hukuncin kotu da ke cewa bangaren gwamnan ke da halastaccen shugaba.

A ranar Alhamis ne dai kotun daukaka kara ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar ga Abdullahi Abbas, kuma sa’o’i da yanke wannan hukuncin uwar jam’iyya ta kasa ta mika masa takardar shaidar shugabanci, matakin da bai yi wa ɓangaren Shekarau dadi ba.

A tattaunawarsa da BBC Hausa, Sanata Ibrahim Shekarau ya ce uwar jam’iyya ta nuna rashin adalci kuma sun yi mamakin irin kalaman da suka fito daga bakin Gwamna Abdullahi Ganduje.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Siyasa

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Published

on

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Jam’iyyar APC reshen Jihar Zamfara ta dakatar da Ɗan Majalisar Wakilai, Aminu Jaji bisa wasu zarge-zargen da ake yi masa na cin amanar jam’iyyar.

Sakataren Yaɗa Labarai na Jam’iyyar APC na Jihar, Malam Yusuf Idris ne ya sanar da dakatarwar a wani taron manema labarai a Gusau a ranar Juma’a.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa, Jaji yana wakiltar mazaɓar Ƙaura-Namoda/Birnin-Magaji a Majalisar Wakilai a ƙarƙashin jam’iyyar APC.

Idris ya ce wasu zarge-zargen da ake yi wa Ɗan Majalisar sun haɗa da aikata rashin gaskiya da rashin zuwa tarurrukan jam’iyyar da kuma sauran ayyuka.

KU KUMA KARANTA: Kotun Najeriya ta bayar da umarnin dakatar da asusun banki fiye da dubu 1

Ya ce, matakin ya biyo bayan sanarwar dakatarwar da aka yi wa Jaji daga shugabannin jam’iyyar APC na mazaɓar Birnin-Magaji bisa zargin cin amanar jam’iyyar da dai sauran abubuwan da suka saɓa wa jam’iyyar.
Idris ya ce, “Kwamitin zartaswa na jam’iyyar APC na ƙaramar hukumar Birnin Magaji ne ya miƙa sanarwar dakatarwar zuwa hedikwatar jam’iyyar APC ta jihar.

Bayanai sun ce kwamitin zartaswar jam’iyyar APC na jihar ya gudanar da taron gaggawa a sakatariyar jam’iyyar da ke Gusau a ranar Juma’a 17 ga watan Mayu, 2024, inda aka gabatar da batun dakatar da Jaji ga ‘yan majalisar zartarwar jihar.

Continue Reading

Labarai

Tsohon gwamnan Katsina, Shema ya sauya sheƙa zuwa APC

Published

on

Tsohon gwamnan jihar Katsina, Ibrahim Shema, a hukumance ya koma jam’iyyar APC Mai mulki a jihar.

Shema, ya kasance gwamnan jihar a tsakanin shekarar 2007 zuwa 2015, a ƙarƙashin jam’iyyar PDP.

Tsohon gwamnan ya yi rajista ne a ofishin jam’iyyar na mazaɓar Shema, ƙaramar hukumar Dutsin-ma, inda shugaban jam’iyyar na jihar, Sani Aliyu-Daura ya ba shi katin zama ɗan jam’iyyar APC.

Lambar katin Shema ta zama ɗan jam’iyyar ita ce: 26551.

KU KUMA KARANTA:Gwamnatin Yobe za ta mayar da kwale-kwalen Dufuna mai shekaru 8,000 zuwa cibiyar yawon buɗe ido

Malam Aliyu-Daura ya yabawa Gwamna Dikko Raɗɗa da kuma tsohon gwamnan jihar Aminu Masari wanda ya gada, a bisa rawar da suka taka wajen ganin Shema ya sauya sheƙa.

Don haka ya tabbatar wa tsohon gwamnan cewa za a yi masa adalci kamar kowane ɗan jam’iyya.

Shugaban ma’aikata na Raɗɗa, Jabiru Abdullahi-Tasuri, shi ne ya miƙa katin zama ɗan jam’iyya ga Shema a madadin gwamnan a jiya Alhamis a Dutsin-ma.

Continue Reading

Labarai

Fusatattun matasa sun lakaɗawa kwamishina duka a wajen zaɓen fidda gwani

Published

on

Banji Ajaka, kwamishinan lafiya na jihar Ondo, ya gamu da fushin matasa a jiya Asabar yayin da ake gudanar da zaɓen fidda gwani na gwamna na jam’iyyar APC mai mulki a jihar.

Daily Trust ta gano cewa Dakta Ajaka, wanda ke Mazaɓar Ugbo 3, a ƙaramar hukumar, ana zarginsa da ɓoye takardar sakamakon zaɓen.

Shaidu sun tabbatar da faruwar lamarin a wata tattaunawa da suka yi da manema labarai, inda suka yi zargin cewa fusatattaun matasan ‘ya’yan jam’iyyar APC ne da ke adawa da tsarin da aka bi wajen gudanar da zaɓen.

Ɗaya daga cikin waɗanda suka shaida lamarin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana cewa rikicin ya faro ne lokacin da ‘yan ɗaya ɓangaren na jam’iyyar suka buƙaci ganin takardar sakamakon zaɓen na fidda gwani.

KU KUMA KARANTA:An yi jana’izar tsohon gwamnan Ondo, Rotimi Akeredolu

“Sun fusata ne suka buƙaci jami’in zaɓe ya ba su takardar sakamakon zaɓen sai kuwa ya ce ta na wajen Ajaka.

“Don haka suka yi masa duka a wurin, inda kuma garinsu ne. Jama’a sun fusata sosai da lamarin, inda rigimar ta ƙare a wajen.”

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Dakta Ajaka ya ce an zarge shi ne da riƙe takardar sakamakon zaɓen.

Ya yi bayanin cewa a lokacin da yake ƙoƙarin bayyana kansa, ’yan daban sun auka masa inda suka yi masa mugun duka.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like