Connect with us

Labari

Ramadan: Wata Cocin Kaduna Ta Raba Buhuhunan Hatsi Ga Musulmai Don Inganta Dangantakar Dake Tsakaninsu

Published

on

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

WATA Cocin Christ Evangelical Intercessory and Life Intervention Ministry da ke Sabon Tasha a Jihar Kaduna ta bayar da gudummawar buhuhunan hatsi iri daban-daban guda 500 ga al’ummar Musulmi a lokacin da suke shirye-shiryen gudanar da azumin watan Ramadan na bana.

Majami’ar ta bayyana cewa an yi amfani da raba nau’in hatsin iri daban-daban ne domin kara samar da zaman lafiya, hadin kai, juriya, soyayya da fahimtar juna a tsakanin mabiya addinan biyu.

Babban mai kula da cocin, Fasto Yohana Buru ya jagoranci tawagar cocin zuwa babban masallacin Juma’a na titin Kano Road a safiyar Juma’a domin bayar da tallafin kayan abinci ga ’yan masallacin.

Ya shaida wa shugabannin masallacin cewa a raba hatsin ga talakawa musulmi, da mabaratan tituna, da marasa galihu da kuma zawarawa.

A cewar sa, an yi hakan ne domin baiwa wadannan Musulman da aka gano domin su samu isasshen abinci a lokacin azumin na kwanaki 30.

Don haka, ya roki Allah Madaukakin Sarki da ya kawo mana karshen matsalolin rashin tsaro da kasar nan da ake fuskanta, musamman a Arewacin kasar nan.

“Wannan shi ne karo na 6 da cocin ke raba buhunan hatsi da sauran kayan abinci ga dimbin mabarata a kan tituna, da ‘yan gudun hijira, da kananan yara a gidajen marayu da kuma talakawa musulmi a cikin al’umma.”

A cewar malamin, “Ramadan din bana na zuwa ne a cikin matsalolin rashin tsaro, tsadar kayan abinci, karancin man fetur, da sauran kayan dafa abinci kamar itacen wuta da gawayi a Jihohin Arewa 19.

An ruwaito cewa Cocin ta raba hatsi, da kayayyakin addu’o’i ga sama da daruruwan musulmi marasa galihu da mabukata wadanda suka hada da matan da mazajensu suka mutu.

‘Dole ne mu tuna cewa mu iyali ɗaya ne a ƙarƙashin Allah, muna bauta wa Allah ɗaya, kuma mun fito daga zuriyar Adamu da Hauwa’u, saboda haka dole ne mu haɗa hannu don tallafa wa juna a kowane yanayi.”

Malamin ya kuma yi kira ga masu hannu da shuni da su rika tunawa da marasa galihu, talakawa, ‘yan gudun hijira da kuma matan da mazansu suka rasu a cikin al’umma domin su samu damar gudanar da Azumin wannan kwanaki 30 cikin sauki.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like