Connect with us

Labari

NUJ Kaduna Ta Gudanar Da Taron Bita, Tare Da Karrama Muyiwa, Isiguzo Da Sauran Su

Published

on

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

KUNGIYAR Yan Jaridu ta Najeriya (NUJ), reshen Jihar Kaduna, ta gudanar da wani taron bita na musamman tare da karrama wasu al’umma da suka hada da mai ba Gwamnan Jihar Kaduna shawara kan harkokin yada labarai, Mista Muyiwa Adekeye, Shugaban Kungiyar (NUJ) ta Najeriya, Kwamared Chris Isiguzo da sauran wasu manyan mutane da lambar yabo bisa gagarumin gudunmuwarsu.

Taron lakcan da bada lambar yabon da ya gudana a ranar Asabar din daya gabata a sakatariyar Kungiyar ta NUJ Kaduna, an shirya ne domin karawa juna sani kan mahimmancin yan Jaridu a cikin harkar Siyasa da irin rawar da zasu taka domin ci gaban Kasar Najeriya.

Da yake jawabi a wajen taron, Shugaban Kungiyar NUJ ta Najeriya, Kwamared Chris Isiguzo, ya bayyana akwai bukatar kasancewar yan Jaridu masu aiki da kwarewa ba tare nuna son rai a cikin aikinsu don tabbatar da an samu sauyi nagari a cikin shugabanci a kasar.

Ya ce “sai da hadin kai da zaman lafiya za a iya samun duk wani ci gaban da ake bukata a cikin kowace al’umma, don haka akwai bukatar yan Jaridu su kasance mutane masu son junansu da kyakkyawar alaka da son zaman lafiya, saboda ta hakan ne zasu iya nuni da ayyukan da za ayi koyi da su.”

“Babu shakka, yan Jaridun Kaduna na matukar Jindadin mulkin shugabancin Kungiyar karkashin Jagorancin Asma’u Yawo Halilu wadda ta yi abubuwa da dama domin inganta rayuwar mambobin kungiyar sakamakon irin hadin kan da suke bats, kuma hakan na nuni da cewa hakkin da ya rataya a wuyan yan Jaridun zasu sauke wannan nauyin ta hanyar gudanar ayyukansu yadda ya kamata.”

Hakazalika, Shugaban taron, Alhaji Ahmed Maiyaki, ya jinjinawa Kungiyar da Jagorancin Asma’u Yawo bisa namijin Kokarin da ta ke na ganin cewa ta daidaita al’amura duk da kasancewar mace kuma ta farko da ta fara rike wannan matsayin a cibiyar kungiyar.

Ya ci gaba da cewa, ba karamin nauyi ba ne yake rataye a wuyan yan Jaridu da za su sauke ta hanyar ganin cewa sun gudanar da ayyukansu a cikin al’umma, musamman a irin wannan lokacin da zabe ke kunno kai kuma yan Siyasa na neman damar da zasu gana da al’umma.

Mai jawabi na musamman a wajen taron, Mista Muyiwa Adekeye, ya bayyana cewa dole ne duk wani dan Jarida da yake son zama yan Jaridu na kwarai, sai sun masu gaskiya, bada rahoton gaskiya da kauracewa yin aiki da jita-jita tare da samarwa da al’umma sahihan labarai na gaskiya.

Ya ce “ada Gwamnatin Jihar Kaduna ba ta da jituwa da Kungiyar ta NUJ Kaduna, amma a yanzu mun dinke gida domin yin aiki tare karkashin Jagorancin Hajiya Asma’u kuma za muyi kokarin ganin cewa an kara daidaita al’amura ta yadda zamu cigaba da gudanar al’amura tare musamman kasancewa Gwamnan yana sha’awar ganin an ba mata dama a cikin kowani mataki.”

Muyiwa Adekeye, ya yaba da ganin irin yadda Kungiyar ta canza salon ta duk da cewa ta na da nauyi kala biyu a kan ta wanda ya hada yin aiki karkashin Kungiyar ma’aikata da Gwamnati wanda hakan wani babban Kalubale ne a gare ta, amma idan ba ta dauki bangaranci yayin gudanar da harkokin ta, duk zata iya samun nasara a cikin ayyukanta.

Tun da farko, shugabar kungiyar (NUJ) ta Kaduna, Kwamared Asma’u Yawo Halilu wadda ta bayyana wasu nasarorin da Kungiyar ta samu a cikin watanni biyar da suka gabata, ya danganta gagarumin ci gaban da aka samu ya zuwa yanzu ga gagarumin goyon bayan da take samu daga mambobin kungiyar da abokan huldar ta.

Ta ci gaba da cewa, sun aiwatar da shirin horarwa don inganta ƙwararrun mambobi tare da haɗin gwiwar ƙungiyoyin jama’a na ci gaba da gudana a jihar.

Ta ce “duk waɗannan nasarorin, an cimma musu ne saboda tallafin da muka samu daga abokan tarayya, masu girma membobinmu kuma tabbas saboda mu ma mun mai da hankali kuma muna da hangen nesa.”

“A yau jagoranmu, Dan Jarida na daya a Najeriya, Kwamared Chris Isiguzo zai kaddamar da dukkan wadannan ayyukan. Namu ne Ina muku barka da zuwa Jihar Kaduna a wannan wata na musamman.”

“Bari kuma in yi amfani da wannan dama don tabbatar wa mambobinmu cewa jindadin ku shi ne mafificin mu. Kamar yadda kuka sani, sana’ar mu tana buƙatar ci gaba da horarwa. Dole ne mu kasance masu horo kafin mu iya sanar da wasu.”- Acewar Asma’u

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like