Connect with us

Siyasa

Ni Ne Wannan Dan Najeriyan Da Ya Kasance Na Kowa Ne A Ko’ina – Sanata Anyim

Published

on

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

TSOHON shugaban majalisar dattawa, Senata Anyim Pius Anyim ya bayyana matsalolin Najeriya a matsayin masu sarkakiya da ke bukatar shugabancin da ya dace ya tunkare su domin kawo Karshen matsalolin da ake fuskanta.

Ayim ya yi wannan magana ne a ranar Litinin yayin da yake jawabi ga wakilan Jam’iyyar PDP a sakatariyar jam’iyyar da ke Kaduna.

Ya kara da cewa matsalolin da ake fuskanta na da bukatar wani jajirtaccen mutum kamar shi domin kowa Karshen abubuwan da ake fuskanta, domin acewar wannan wani abu ne daya taba yi a lokacin da yake rike da shugabancin Majalisar Dattawa a matsayin Shugaba.

Ya ce “ni ne wannan dan Najeriyan da tun da nake a rayuwata ban taba tafiya na bar kasar nan sama da sati biyu, kuma yara na a kasar nan suke karatu kuma wannan dan Najeriyan da ya kasance na kowa ne a ko’ina.”

“Idan muna da shugabanci nagari, komai zai yi daidai, kuma ni ne wannan Shugaban wanda Kasar Najeriya nan ta ke bukata, kuma idan kuka tura ni a wannan aiken, zan dawo muku da irin kyakkyawar tsohuwar rayuwar da kuka saba da ita ada.”

“Yau a Najeriya mutane da yawa za su fito su ware rashin tsaro, wasu kuma za su ware tattalin arziki, amma zan iya fada muku cewa matsalolinmu suna da sarkakiya, wani kuma yana haifar da wani.

“Idan ka tambaye ni, kalubalen da ke gabanmu a yanzu shi ne samun ingantaccen shugabanci wanda ya san matsalolin da yadda za a gyara matsalolin,” Anyim ya bayyana.

Ya tuna cewa ya shafe shekaru 33 yana aikin gwamnati.

“Na kasance a kusa da gwamnati da shugaban kasa; Na yi aiki a matsayin Sanata; Na taba zama shugaban majalisar dattawa.

“A lokacin da aka fi fama da rikici a waccan majalisar dattijai lokacin da na zo, na sake haduwa da kowa kuma rikicin ya ragu,” inji shi.

Ayim ya ci gaba da cewa Najeriya na bukatar shugaba irinsa ya fito ta hanyar fahimtar juna da nufin magance kalubalen kowace kungiya ko bangaren kasar nan domin samun zaman lafiya.

“Aikina ne, na yi alƙawarin cewa idan kun ba ni dama, za mu yi aiki tare, mu mai da Najeriya yadda muke so ta zama.

“Mai gina kasa ne kadai zai iya karfafa kafuwar kasarmu, kuma an fara zabar mutumin da zai jagoranci Najeriya zuwa ga wadata da tsaro,” in ji Ayim.

A cikin sakon nasa na fatan alheri, Sen. Ahmad Makarfi ya bayyana Sanata Ayim a matsayin daya daga cikin jiga-jigan ‘yan takarar jam’iyyar, tare da yi masa fatan samun nasara gabanin zaben fidda gwani na jam’iyyar.

Sanata Anyim ya rike mukamin shugaban majalisar dattawa daga shekarar 2000 zuwa 2003, da kuma sakataren gwamnatin tarayya daga shekarar 2011 zuwa 2015.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Siyasa

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Published

on

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Jam’iyyar APC reshen Jihar Zamfara ta dakatar da Ɗan Majalisar Wakilai, Aminu Jaji bisa wasu zarge-zargen da ake yi masa na cin amanar jam’iyyar.

Sakataren Yaɗa Labarai na Jam’iyyar APC na Jihar, Malam Yusuf Idris ne ya sanar da dakatarwar a wani taron manema labarai a Gusau a ranar Juma’a.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa, Jaji yana wakiltar mazaɓar Ƙaura-Namoda/Birnin-Magaji a Majalisar Wakilai a ƙarƙashin jam’iyyar APC.

Idris ya ce wasu zarge-zargen da ake yi wa Ɗan Majalisar sun haɗa da aikata rashin gaskiya da rashin zuwa tarurrukan jam’iyyar da kuma sauran ayyuka.

KU KUMA KARANTA: Kotun Najeriya ta bayar da umarnin dakatar da asusun banki fiye da dubu 1

Ya ce, matakin ya biyo bayan sanarwar dakatarwar da aka yi wa Jaji daga shugabannin jam’iyyar APC na mazaɓar Birnin-Magaji bisa zargin cin amanar jam’iyyar da dai sauran abubuwan da suka saɓa wa jam’iyyar.
Idris ya ce, “Kwamitin zartaswa na jam’iyyar APC na ƙaramar hukumar Birnin Magaji ne ya miƙa sanarwar dakatarwar zuwa hedikwatar jam’iyyar APC ta jihar.

Bayanai sun ce kwamitin zartaswar jam’iyyar APC na jihar ya gudanar da taron gaggawa a sakatariyar jam’iyyar da ke Gusau a ranar Juma’a 17 ga watan Mayu, 2024, inda aka gabatar da batun dakatar da Jaji ga ‘yan majalisar zartarwar jihar.

Continue Reading

Labarai

Tsohon gwamnan Katsina, Shema ya sauya sheƙa zuwa APC

Published

on

Tsohon gwamnan jihar Katsina, Ibrahim Shema, a hukumance ya koma jam’iyyar APC Mai mulki a jihar.

Shema, ya kasance gwamnan jihar a tsakanin shekarar 2007 zuwa 2015, a ƙarƙashin jam’iyyar PDP.

Tsohon gwamnan ya yi rajista ne a ofishin jam’iyyar na mazaɓar Shema, ƙaramar hukumar Dutsin-ma, inda shugaban jam’iyyar na jihar, Sani Aliyu-Daura ya ba shi katin zama ɗan jam’iyyar APC.

Lambar katin Shema ta zama ɗan jam’iyyar ita ce: 26551.

KU KUMA KARANTA:Gwamnatin Yobe za ta mayar da kwale-kwalen Dufuna mai shekaru 8,000 zuwa cibiyar yawon buɗe ido

Malam Aliyu-Daura ya yabawa Gwamna Dikko Raɗɗa da kuma tsohon gwamnan jihar Aminu Masari wanda ya gada, a bisa rawar da suka taka wajen ganin Shema ya sauya sheƙa.

Don haka ya tabbatar wa tsohon gwamnan cewa za a yi masa adalci kamar kowane ɗan jam’iyya.

Shugaban ma’aikata na Raɗɗa, Jabiru Abdullahi-Tasuri, shi ne ya miƙa katin zama ɗan jam’iyya ga Shema a madadin gwamnan a jiya Alhamis a Dutsin-ma.

Continue Reading

Labarai

Fusatattun matasa sun lakaɗawa kwamishina duka a wajen zaɓen fidda gwani

Published

on

Banji Ajaka, kwamishinan lafiya na jihar Ondo, ya gamu da fushin matasa a jiya Asabar yayin da ake gudanar da zaɓen fidda gwani na gwamna na jam’iyyar APC mai mulki a jihar.

Daily Trust ta gano cewa Dakta Ajaka, wanda ke Mazaɓar Ugbo 3, a ƙaramar hukumar, ana zarginsa da ɓoye takardar sakamakon zaɓen.

Shaidu sun tabbatar da faruwar lamarin a wata tattaunawa da suka yi da manema labarai, inda suka yi zargin cewa fusatattaun matasan ‘ya’yan jam’iyyar APC ne da ke adawa da tsarin da aka bi wajen gudanar da zaɓen.

Ɗaya daga cikin waɗanda suka shaida lamarin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana cewa rikicin ya faro ne lokacin da ‘yan ɗaya ɓangaren na jam’iyyar suka buƙaci ganin takardar sakamakon zaɓen na fidda gwani.

KU KUMA KARANTA:An yi jana’izar tsohon gwamnan Ondo, Rotimi Akeredolu

“Sun fusata ne suka buƙaci jami’in zaɓe ya ba su takardar sakamakon zaɓen sai kuwa ya ce ta na wajen Ajaka.

“Don haka suka yi masa duka a wurin, inda kuma garinsu ne. Jama’a sun fusata sosai da lamarin, inda rigimar ta ƙare a wajen.”

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Dakta Ajaka ya ce an zarge shi ne da riƙe takardar sakamakon zaɓen.

Ya yi bayanin cewa a lokacin da yake ƙoƙarin bayyana kansa, ’yan daban sun auka masa inda suka yi masa mugun duka.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like