Connect with us

Labari

Mun Gamsu Da Ayyukan Da El-Rufa’i Ya Shimfida A Kaduna- Inji Aminu Rahama

Published

on

Daga; Rabo Haladu, Kaduna.

DAN majalisar dokokin Jihar Kaduna Mai wakiltar mazabar Karamar hukumar MaKarfi a zauren majalisar Jihar, Aminu Ahmad Rahama, ya bayyana gamsuwarsa dangane da irin ayyukan da gwamnan Jihar Malam Nasiru Ahmed El-rufa’i ya shimfida a Jihar a cikin shekaru shida da ya yi a kan kujerar gwamna Jihar.

Aminu Ahmad Rahama, ya ce al’ummar Jihar Kaduna suna alfahari da ayyukan ci gaba da gwamnatin APC a Jihar ta kawo wanda al’umma ba za su manta da gudunmuwar da Gwamna El-rufa’i ya kawo a Jihar baki daya ba.

Dan majalisar ya bayyana haka ne a jawabinsa yayin da kungiyar ‘yan jarida na Arewa suka karramashi da lambar yabo bisa gudunmuwar da ya kawo a mazabarsa na tallafawa al’umma.

Aminu Rahama, ya kara da cewa, duk kudurorin da gwamna yake aikowa majalisa; kudurorine na bunkasa ci gaban Jihar ne wanda hakan ya sanya ba a samun baraka tsakanin bangaren zartaswa dana majalisar Jihar. A cewarsa, sun gamsu da ayyukan ci gaba da gwamnatin Jihar take shimfidawa a ciki da wajen Jihar baki daya.

A cewar dan majalisar, Gwamna Nasir El-Rufai ya gina kuma yana ci gaba da gina ababen more rayuwa a Jihar Kaduna yana mai cewa ya kafa ma’auni masu girma wanda dole ne a tabbatar da cewa an kiyaye tare da kiyaye abubuwan more rayuwa da ya gina.

Ya ce “ya zama wajibi su bawa jagoransu kwarin gwiwa da ya ci gaba a yunkurin ganin Jihar Kaduna ta zama abin koyi na ci gaba a fadin kasar baki daya.”

Dan majalisar ya bukaci daukacin al’ummar Jihar dasu taimakawa kokarin Gwamnatin Jihar na samar da zaman lafiya a fadin Jihar wanda sai da zaman lafiya ci gaba zai kara samuwa.

A kan hakan, yace matsayinsu na wakilan al’ummar Jihar kuma masu tsara dokoki, za su yi iya bakin kokarinsu wajen samar da dokokin da zasu kawo ci gaba a Jihar, hasalima, zasu ci gaba da zama wakilai na gari a zauren majalisar Jihar.

Daga karshe, ya yaba da kokarin kafafen yada labarai wajen bayyanawa al’umma halin da kasa take ciki inda ya bukace dasu kaucewa yada labaran da zasu kawo rashin zaman lafiya a kasa baki daya.

Ni ɗan jarida ne mai zaman kansa. Mawallafi kuma mai sharhi a lamarin yau da kullum.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like