Labarai
Malamai su daina tsine wa Najeriya, su ke yi mata addu’a — Tinubu
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/03/20240329_052726.jpg)
Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya yi ƙira ga shugabannin addini da su daina tsine wa Najeriya a tarukansu ko wa’azi.
Tinubu ya bayyana haka ne a Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja a ranar Alhamis, yayin buɗa-baki da malaman addinai da masu sarautun gargajiya.
“A ranar Laraba na halarci jana’izar sojoji 17 da aka kashe a Okuama, Jihar Delta. Na ga matansu masu ciki da yara ƙanana.
”Soyayyar al’umma tana hannunku. Ku yi wa kasarmu addu’a. Ku bai wa yaranmu ilimi da tarbiyya. Wa’azin da muke yi wa mutane a coci da masallatai suna da muhimmanci.
“Kada ku la’anci al’ummarku. Wannan ita ce ƙasarku; kar a yi Allah-wadai da ita a cikin wa’azi, kada ku zagi ƙasar nan. Shugabanci na nufin kawo sauyi.
“A ce wannan shugaban ba shi da kirki, wannan ba laifi ba ne. Amma ku bari sai zabe na gaba sai ku sauya shi, amma ku daina la’antar kasar nan. Kar ku zagi Najeriya. Wannan kyakkyawar kasa ce.”
KU KUMA KARANTA: Tinubu ya karrama sojojin da aka kashe a Delta
Shugaban ya nusar da su muhimmancin sauya akidun mutane, ta hanyar cusa musu kishin kasa da dora su a hanya mafi dacewa.
Tinubu, ya buƙaci shugabannin addinai da suka kasance masu adalci wajen sukar masu rike da mukaman siyasa.
A gefe guda kuma, Tinubu ya jadadda wa shugabannin aniyarsa ta magance ɗimbin matsalolin da ake fuskanta a ƙasar nan nan.
Taron buɗa-bakin ya samu halartar sarakunan gargajiya daga Arewaci da Kudancin Najeriya da kuma malaman addinin Musulunci da na Kirista.
Shugaban Tinubu ya kuma buƙaci shugabannin gargajiya da na addinai da su kulla alaƙa mai ƙarfi da gwamnati domin kawo ƙarshen ayyukan ta’addanci da sauran laifuka a ƙasar nan.
Mahalarta taron sun yaba wa Tinubu kan salon mulkinsa da kuma yadda yake jajircewa wajen kawo wa Najeriya sauyi mai ɗorewa.
Labarai
Sarkin Gwandu ya naɗa ɗan Buran ɗin Gwandu babba
![Sarkin Gwandu ya naɗa ɗan Buran ɗin Gwandu babba](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/07/IMG-20240726-WA0012.jpg)
Sarkin Gwandu ya naɗa ɗan Buran ɗin Gwandu babba
Daga Haruna Abdulrashid
Shugaban majalisar sarakuna ta jihar Kebbi, Mai martaba Sarkin Gwandu, Manjo-Janar Muhammadu Ilyasu Bashar Mni, ya karrama Shugaban hukumar jin daɗi da walwalar Alhazzai ta ƙasa, Malam Jalal Muhammad Arabi da sarautar (ƊAN BURAN GWANDU BABBA) inda mai martaba sarki ya aike da tawaga zuwa birnin tarayya Abuja domin gabatar da wannan karramawa zuwa ga Malam Jalal Arabi.
Da ya ke jawabi a madadin mai martaba sarkin Gwandu Alhaji Aminu Ahmad, Sarkin Fadan Gwandu ya bayyana cewa mai martaba sarkin Gwandu ya amince da bayar da wannan karramawa ga Malam Jalal ne a bisa jajircewa da kuma taimako da yake yiwa Alhazzan Najeriya tare da haɗin kai da yake bawa shugabanni a kan abin da ya shafi harkar aikin Hajji mussaman a bana.
Shi ma shugaban hukumar jin daɗin da walwalar Alhazai ta jihar Kebbi, Alhaji Faruƙu Musa Yaro Enabo, Jagaban Gwandu, ya bayyana jin daɗin shi matuƙa a kan wannan karramawar da aka yi wa maigidan shi.
Ya kuma yabawa mai martaba Sarkin Gwandu Manjo-Janar Muhammadu Ilyasu Bashar akan yadda yake gabatar da kyakkyawan jagoranci zuwa ga Al’ummar Gwandu.
Wannan bayar da takardar karramawa ta sarautar (ƊAN BURAN GWANDU) Sun haɗa da Alh Aminu Ahmed Sarkin Fadan Gwandu, Alh Aminu Abubakar Gulumbe Uban ƙasar Gulumbe, Alh. Mustapha Ka’oje Sarkin Bargun Ka’oje, Alh Lamiru Shehu Sakataren Sarakunan jihar Kebbi, Alh Faruƙu Musa Yaro Enabo Jagaban Gwandu, Alh Usman Osho da Alh Rilwanu Awwal.
Mai girma Shugaban hukumar Jin daɗi da walwalar Alhazzai ta jihar Kebbi, Malam Jalal Arabi, ya bayyana jin daɗin shi sosai ganin wanan karramawa da ya samu daga masarautar Gwandu.
Ya kuma ce jihar Kebbi ta zama gida a gareshi ganin yadda yake samun karramawa da mutuntawa a jihar ya kuma bayyana mana irin mutunci da zumunci dake tsakanin shi da shugaban hukumar Jin daɗi da walwalar Alhazzai ta jihar Kebbi.
Alh Faruku Musa Yaro Enabo Jagaban Gwandu ya kuma yi godiya da jinjina zuwa ga Maigirma Gwamnan jihar Kebbi His Excellency Comrd Dr. Nasir Idris Ƙauran Gwandu akan irin yadda yayi ɗawainiya ga Alhazzan jihar shi.
Labarai
Mun gana da shugaba Tinubu mun isar masa saƙon al’umma – Shaikh Bala Lau
![Mun gana da shugaba Tinubu mun isar masa saƙon al'umma - Shaikh Bala Lau](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/07/IMG-20240726-WA0011.jpg)
Mun gana da shugaba Tinubu mun isar masa saƙon al’umma – Shaikh Bala Lau
Daga Idris Umar, Zariya
A ranar Alhamis tawagar malaman Najeriya ta gana da shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu dangane da halin da ƙasa ta ke ciki kan batun zanga-zanga da wasu ke ƙiran a yi dalilin halin matsi da tsadar rayuwa.
Rahoton sun nuna cewa jim kaɗanne bayan kammala ganawar, shugaban ƙungiyar Izala na ƙasa, Shaikh Abdullahi Bala Lau ya shaidawa manema labarai cewa shugaban ƙasa ya karɓi koken da suka je masa da shi.
“Mun faɗa mar halin da al’umma suke ciki na tsadar rayuwa, taɓarɓarewar tsaro da wahalar rayuwa, ya kuma ce dan Allah a ja hankalin al’umma a ba su haƙuri nan gaba kaɗan za a ga sauyi da gyara kan ƙorafe-ƙorafen da ake yi”. In ji Bala Lau.
KU KUMA KARANTA: Zanga-zanga ba gudu ba ja da baya – ‘Yan Najeriya
Daga nan kuma, Shaikh ɗin ya ja hankalin al’umma da su yi haƙuri su cigaba da addu’a, “ba mu da ƙasar da ta fi Najeriya kar mu rusa ƙasarmu da kanmu”. Inji Shaikh Bala Lau.
Ilimi
Gwamnatin Katsina ta jaddada manufarta na ci gaba da bayar da horo ga malaman makaranta
![Gwamnatin Katsina ta jaddada manufarta na ci gaba da bayar da horo ga malaman makaranta](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/07/IMG-20240726-WA0008.jpg)
Gwamnatin Katsina ta jaddada manufarta na ci gaba da bayar da horo ga malaman makaranta
Daga Idris Umar, Zariya
Kwamishinar kula da ilimin firamare da na Sakandire ne ta bayyana ƙudirin gwamnatin jihar mai ci yanzu na ci gaba da bayar da ƙarin horo ga malamai a faɗin jihar don samar da ƙwararrun malamai da suka iya sarrafa na’ura mai ƙwaƙwalwa da za su yi gogayya da takwarorinsu a faɗin duniya.
Hajiya Zainab Musa Musawa ta bayar da tabbacin hakan ne a lokacin da ta kai ziyarar duba yadda shirin horar da malamai 10,000 da suka haɗa da sabbin ɗauka 7,000 a kan dabarun koyarwa na ƙarni na 20 ke gudana.
Kwamishinar ta kai ziyarar ne a makarantar firamare ta Modoji inda ake gudanar da bayar da horon na yini 3 wanda Ma’aikatar kula da ilimin firamare da na Sakandire, hukumar ilimin bai ɗaya da kuma haɗin gwiwa da shirin bunƙasa ilimi matakin jiha (TESS) suka shirya.
KU KUMA KARANTA: Da ilimi ake samun kowace irin nasara a rayuwa – Dauda Lawal
Hajiya Zainab Musa Musawa wanda ta zagaya azuzuwa ta kuma tattauna da masu bayar da horon da Kuma malaman, ta bukace su da suyi amfani da lokacin su fahimci Abunda aka koyamasu don bunkasa tsarin koyo da koyarwa a jihar.
A yayin ziyarar dai Kwamishinar ta samu rakiyar Babbar Sakatariya a Ma’aikatar Hajiya Mairo Mohamed Othman, Mai baiwa Gwamna shawarma akan ilimi Nura Sale Katsayal sauran Daraktocin Ma’aikatar.
Bayanin hakan na ƙunshe a cikin wata sanarwa wadda jami’in hudda da jama’a na Ma’aikatar Malam Sani Ɗanjuma Suleiman ya Sanyama hannu a katsina.
-
Kotu1 year ago
Kotu tayi watsi da ƙarar APC game da zaɓen Abba Gida Gida
-
Labarai10 months ago
Dalilin da ya sa na saka wa matata sasari – Wani magidanci a Potiskum
-
Ƙasashen Waje1 year ago
Ɗaliban Najeriya a Sudan sun nemi a kwaso su daga ƙasar
-
Labarai1 year ago
‘Yan banga sun kama wani mutum da ke yunƙurin sace yarinya a Kano