Connect with us

Siyasa

Ku Tabbatar Kun Zabi ‘Yan Takarar Da Suka Dace – Atiku Ga Wakilan PDP Kaduna

Published

on

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

TSOHON mataimakin Shugaban Kasar Najeriya kuma dan takarar Shugabancin Kasar a karkashin Jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar, ya buƙaci masu zaben yan takara a Jihar Kaduna da su yi kokarin tabbatar da sun zabi Jajirtattun mutane wadanda zasu tsayar takara a zaben fidda gwani na Jam’iyyar da zai gudana.

Dan takarar Atiku Abubakar, ya bayyana hakan ne a garin Kaduna a ranar talata yayin ganawa da wakilan Jam’iyyar PDP masu zaben yan takarar Jam’iyyar, inda ya furta cewa yana da yakinin Jam’iyyar ce ta yi nasara a zaben shekarar 2015 da 2019 a Jihar da kasar baki daya.

Ya kara da cewa Jihar Kaduna gida ne a gare shi kuma a yanzu ya zo gida ne domin ganawa da yan uwan shi kuma ya nemi goyon bayan ‘ya’yan Jam’iyyar tare da wakilan domin tabbatar da tsayar da shi a matsayin dan takarar shugaban kasa a tutar Jam’iyyar.

Ya ce ” a PDP na ci zabe a shekarar 2019 amma aka kwace mana har da nan Jihar Kaduna, amma wannan karon muna son ku kare, ku tsare don haka yasa muka sake dawowa neman goyon bayan ku na sake tsayawa takara a wannan karon.”

“Na dauki alkawarin maganin wannan bala’in da Jam’iyyar APC ta kawo mana na talauci, rashin tsaro, rashin aikin yi da yunwa, don haka mun dauki alkawarin dawo muku da zaman lafiya, tsaro da kwanciyar hankali idan kuka zabe mu.”

“Wadannan na daga cikin kudirori biyar da nayi alkawarin kamar yadda na fada a garin Abuja, sannan zan zauna da yan Majalisu, Gwamnoni da Wakilanmu domin tabbatar da an shirya tsare-tsaren ba kananan hukumomi yancinsu, kana da warware matsalar Kungiyar malaman Jami’o’i.”

Tsohon mataimakin Shugaban Kasar, kuma Wazirin Adamawa, Atiku Abubakar ya jinjinawa al’ummar Jihar ta Kaduna da wakilan Jam’iyyar bisa kokarin da suke na ganin cewa sun tsayar da yan takarar nagari a zaben fidda gwani da za a gudanar nan da wasu yan kwanaki.

Da yake jawabi a madadin Dattawan Jam’iyyar, tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, kuma tsohon Shugaban riko na Jam’iyyar, Sanata Ahmad Makarfi, ya ce dan takarar haziki ne wanda ya cancanci zama Shugaban Kasar Najeriya don haka basa shakka a kan burinsa.

Ya kara da cewa ya zame masu wajibi su zo su tare shi jin cewa zai zo domin Jihar Kaduna garin ne wanda hakan ya sanya barin garin Abuja domin zuwa ya tarbe shi da tsohon Gwamnan Jihar Muktar Ramalan Yero, tare da tsohon Sanatan Shiyyar Kaduna ta tsakiya Kwamared Shehu Sani.

Hakazalika da jake jawabin maraba ga Dan takarar, Shugaban Jam’iyyar PDP ta Jihar Kaduna, Honarabul Hassan Hyet, ya bayyana cewa wannan wani nauyi ne ya rataya a wuyansu na ganin cewa sun tabbatar da ba shi goyon bayan domin shi cikakken dan Jihar Kaduna, illa Jihar Adamawa Kasar shi ce ta haihu kawai.

Shugaban Jam’iyyar, ya yiwa Dan takarar fatan alheri na samun nasara tare da yin alkawarin Kokarin ganin duk wakilan Jam’iyyar sun zabe shi a zaben fidda gwani na Jam’iyyar.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Siyasa

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Published

on

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Jam’iyyar APC reshen Jihar Zamfara ta dakatar da Ɗan Majalisar Wakilai, Aminu Jaji bisa wasu zarge-zargen da ake yi masa na cin amanar jam’iyyar.

Sakataren Yaɗa Labarai na Jam’iyyar APC na Jihar, Malam Yusuf Idris ne ya sanar da dakatarwar a wani taron manema labarai a Gusau a ranar Juma’a.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa, Jaji yana wakiltar mazaɓar Ƙaura-Namoda/Birnin-Magaji a Majalisar Wakilai a ƙarƙashin jam’iyyar APC.

Idris ya ce wasu zarge-zargen da ake yi wa Ɗan Majalisar sun haɗa da aikata rashin gaskiya da rashin zuwa tarurrukan jam’iyyar da kuma sauran ayyuka.

KU KUMA KARANTA: Kotun Najeriya ta bayar da umarnin dakatar da asusun banki fiye da dubu 1

Ya ce, matakin ya biyo bayan sanarwar dakatarwar da aka yi wa Jaji daga shugabannin jam’iyyar APC na mazaɓar Birnin-Magaji bisa zargin cin amanar jam’iyyar da dai sauran abubuwan da suka saɓa wa jam’iyyar.
Idris ya ce, “Kwamitin zartaswa na jam’iyyar APC na ƙaramar hukumar Birnin Magaji ne ya miƙa sanarwar dakatarwar zuwa hedikwatar jam’iyyar APC ta jihar.

Bayanai sun ce kwamitin zartaswar jam’iyyar APC na jihar ya gudanar da taron gaggawa a sakatariyar jam’iyyar da ke Gusau a ranar Juma’a 17 ga watan Mayu, 2024, inda aka gabatar da batun dakatar da Jaji ga ‘yan majalisar zartarwar jihar.

Continue Reading

Labarai

Tsohon gwamnan Katsina, Shema ya sauya sheƙa zuwa APC

Published

on

Tsohon gwamnan jihar Katsina, Ibrahim Shema, a hukumance ya koma jam’iyyar APC Mai mulki a jihar.

Shema, ya kasance gwamnan jihar a tsakanin shekarar 2007 zuwa 2015, a ƙarƙashin jam’iyyar PDP.

Tsohon gwamnan ya yi rajista ne a ofishin jam’iyyar na mazaɓar Shema, ƙaramar hukumar Dutsin-ma, inda shugaban jam’iyyar na jihar, Sani Aliyu-Daura ya ba shi katin zama ɗan jam’iyyar APC.

Lambar katin Shema ta zama ɗan jam’iyyar ita ce: 26551.

KU KUMA KARANTA:Gwamnatin Yobe za ta mayar da kwale-kwalen Dufuna mai shekaru 8,000 zuwa cibiyar yawon buɗe ido

Malam Aliyu-Daura ya yabawa Gwamna Dikko Raɗɗa da kuma tsohon gwamnan jihar Aminu Masari wanda ya gada, a bisa rawar da suka taka wajen ganin Shema ya sauya sheƙa.

Don haka ya tabbatar wa tsohon gwamnan cewa za a yi masa adalci kamar kowane ɗan jam’iyya.

Shugaban ma’aikata na Raɗɗa, Jabiru Abdullahi-Tasuri, shi ne ya miƙa katin zama ɗan jam’iyya ga Shema a madadin gwamnan a jiya Alhamis a Dutsin-ma.

Continue Reading

Labarai

Fusatattun matasa sun lakaɗawa kwamishina duka a wajen zaɓen fidda gwani

Published

on

Banji Ajaka, kwamishinan lafiya na jihar Ondo, ya gamu da fushin matasa a jiya Asabar yayin da ake gudanar da zaɓen fidda gwani na gwamna na jam’iyyar APC mai mulki a jihar.

Daily Trust ta gano cewa Dakta Ajaka, wanda ke Mazaɓar Ugbo 3, a ƙaramar hukumar, ana zarginsa da ɓoye takardar sakamakon zaɓen.

Shaidu sun tabbatar da faruwar lamarin a wata tattaunawa da suka yi da manema labarai, inda suka yi zargin cewa fusatattaun matasan ‘ya’yan jam’iyyar APC ne da ke adawa da tsarin da aka bi wajen gudanar da zaɓen.

Ɗaya daga cikin waɗanda suka shaida lamarin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana cewa rikicin ya faro ne lokacin da ‘yan ɗaya ɓangaren na jam’iyyar suka buƙaci ganin takardar sakamakon zaɓen na fidda gwani.

KU KUMA KARANTA:An yi jana’izar tsohon gwamnan Ondo, Rotimi Akeredolu

“Sun fusata ne suka buƙaci jami’in zaɓe ya ba su takardar sakamakon zaɓen sai kuwa ya ce ta na wajen Ajaka.

“Don haka suka yi masa duka a wurin, inda kuma garinsu ne. Jama’a sun fusata sosai da lamarin, inda rigimar ta ƙare a wajen.”

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Dakta Ajaka ya ce an zarge shi ne da riƙe takardar sakamakon zaɓen.

Ya yi bayanin cewa a lokacin da yake ƙoƙarin bayyana kansa, ’yan daban sun auka masa inda suka yi masa mugun duka.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like