Connect with us

Siyasa

Kaduna 2023: Ni Ne Mafi Cancantar Zama Dan Takarar Gwamna A PDP – Ramalan Yero

Published

on

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

TSOHON Gwamnan Jihar Kaduna, Mukhtar Ramalan Yero, a ranar Juma’a ya bayyana kansa a matsayin wanda ya fi kowa kwarewa da kwarin guiwa wajen neman tikitin takarar gwamna a jam’iyyar People’s Democratic Party (PDP) gabanin zaben 2023 a Jihar.

Tsohon gwamnan wanda ya kasance a sakatariyar jam’iyyar a ranar Juma’a 20 ga watan Mayu, 2022, ya shaida wa shugabannin jam’iyyar PDP da masu son tsayawa takara su tuna da tarihin siyasarsa da abin da ya iya yi a lokacin da ya yi wa jihar hidima a wurare daban-daban, inda ya bukace su fara yin la’akari da shi a lokacin zaben fidda gwani da za a yi a jihar.

Ya ce “idan aka yi la’akari da irin abubuwan da ya faru a baya da kuma kokarin da na yi a matsayinna na tsohon ma’aikacin gidan Sir Ibrahim Kashim da kuma sabbin ilimin da ya karawa a cikin shekaru bakwai da suka wuce, zai iya magance tattalin arziki, lafiya, ilimi, kawo hadin kai, jin dadin ‘yan kasa da kawar da sauran kalubalen da ke kawo cikas a jihar idan aka sake ba shi dama.

Da yake jawabi ga manema labarai jim kadan bayan ziyarar da suka kai a sakatariyar jam’iyyar, kwararren masani kan harkokin kudi ya ce, “a yau mun samu damar ziyartar ofishin babbar jam’iyyar mu da ke cikin babban birninmu na Kaduna, domin mu kara kusantar shugabanni da masu kishin kasa kan burinmu na niyyar tsayawa takarar gwamna a karkashin jam’iyyar.

“Na shaida musu cewa ni gwamna ne a baya kuma na yi wa jihar hidima a wurare daban-daban wanda hakan ke nufin ni ba bako bane a jam’iyyar da jama’armu a jihar.

“Saboda halin da muka tsinci kanmu a yau da kuma kasa baki daya kamar kalubalen tsaro, tattalin arziki, ilimi, lafiya, hadin kai da jin dadin jama’a, sai muka ji cewa wasu daga cikinmu da suke can a da kuma suna iya yin aikin sun ga bukatar hakan domin mu zo mu magance wadannan kalubale domin mu samu kwanciyar hankali da wadata.

“Don haka na zo ne domin in sanar da jam’iyyar cewa ina cikin takara sannan in yi kira ga shugabannin jam’iyyar da wakilan jam’iyyar su duba abin da muka yi da abin da za mu iya yi idan aka ba mu dama”. Ya ce.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Siyasa

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Published

on

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Jam’iyyar APC reshen Jihar Zamfara ta dakatar da Ɗan Majalisar Wakilai, Aminu Jaji bisa wasu zarge-zargen da ake yi masa na cin amanar jam’iyyar.

Sakataren Yaɗa Labarai na Jam’iyyar APC na Jihar, Malam Yusuf Idris ne ya sanar da dakatarwar a wani taron manema labarai a Gusau a ranar Juma’a.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa, Jaji yana wakiltar mazaɓar Ƙaura-Namoda/Birnin-Magaji a Majalisar Wakilai a ƙarƙashin jam’iyyar APC.

Idris ya ce wasu zarge-zargen da ake yi wa Ɗan Majalisar sun haɗa da aikata rashin gaskiya da rashin zuwa tarurrukan jam’iyyar da kuma sauran ayyuka.

KU KUMA KARANTA: Kotun Najeriya ta bayar da umarnin dakatar da asusun banki fiye da dubu 1

Ya ce, matakin ya biyo bayan sanarwar dakatarwar da aka yi wa Jaji daga shugabannin jam’iyyar APC na mazaɓar Birnin-Magaji bisa zargin cin amanar jam’iyyar da dai sauran abubuwan da suka saɓa wa jam’iyyar.
Idris ya ce, “Kwamitin zartaswa na jam’iyyar APC na ƙaramar hukumar Birnin Magaji ne ya miƙa sanarwar dakatarwar zuwa hedikwatar jam’iyyar APC ta jihar.

Bayanai sun ce kwamitin zartaswar jam’iyyar APC na jihar ya gudanar da taron gaggawa a sakatariyar jam’iyyar da ke Gusau a ranar Juma’a 17 ga watan Mayu, 2024, inda aka gabatar da batun dakatar da Jaji ga ‘yan majalisar zartarwar jihar.

Continue Reading

Labarai

Tsohon gwamnan Katsina, Shema ya sauya sheƙa zuwa APC

Published

on

Tsohon gwamnan jihar Katsina, Ibrahim Shema, a hukumance ya koma jam’iyyar APC Mai mulki a jihar.

Shema, ya kasance gwamnan jihar a tsakanin shekarar 2007 zuwa 2015, a ƙarƙashin jam’iyyar PDP.

Tsohon gwamnan ya yi rajista ne a ofishin jam’iyyar na mazaɓar Shema, ƙaramar hukumar Dutsin-ma, inda shugaban jam’iyyar na jihar, Sani Aliyu-Daura ya ba shi katin zama ɗan jam’iyyar APC.

Lambar katin Shema ta zama ɗan jam’iyyar ita ce: 26551.

KU KUMA KARANTA:Gwamnatin Yobe za ta mayar da kwale-kwalen Dufuna mai shekaru 8,000 zuwa cibiyar yawon buɗe ido

Malam Aliyu-Daura ya yabawa Gwamna Dikko Raɗɗa da kuma tsohon gwamnan jihar Aminu Masari wanda ya gada, a bisa rawar da suka taka wajen ganin Shema ya sauya sheƙa.

Don haka ya tabbatar wa tsohon gwamnan cewa za a yi masa adalci kamar kowane ɗan jam’iyya.

Shugaban ma’aikata na Raɗɗa, Jabiru Abdullahi-Tasuri, shi ne ya miƙa katin zama ɗan jam’iyya ga Shema a madadin gwamnan a jiya Alhamis a Dutsin-ma.

Continue Reading

Labarai

Fusatattun matasa sun lakaɗawa kwamishina duka a wajen zaɓen fidda gwani

Published

on

Banji Ajaka, kwamishinan lafiya na jihar Ondo, ya gamu da fushin matasa a jiya Asabar yayin da ake gudanar da zaɓen fidda gwani na gwamna na jam’iyyar APC mai mulki a jihar.

Daily Trust ta gano cewa Dakta Ajaka, wanda ke Mazaɓar Ugbo 3, a ƙaramar hukumar, ana zarginsa da ɓoye takardar sakamakon zaɓen.

Shaidu sun tabbatar da faruwar lamarin a wata tattaunawa da suka yi da manema labarai, inda suka yi zargin cewa fusatattaun matasan ‘ya’yan jam’iyyar APC ne da ke adawa da tsarin da aka bi wajen gudanar da zaɓen.

Ɗaya daga cikin waɗanda suka shaida lamarin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana cewa rikicin ya faro ne lokacin da ‘yan ɗaya ɓangaren na jam’iyyar suka buƙaci ganin takardar sakamakon zaɓen na fidda gwani.

KU KUMA KARANTA:An yi jana’izar tsohon gwamnan Ondo, Rotimi Akeredolu

“Sun fusata ne suka buƙaci jami’in zaɓe ya ba su takardar sakamakon zaɓen sai kuwa ya ce ta na wajen Ajaka.

“Don haka suka yi masa duka a wurin, inda kuma garinsu ne. Jama’a sun fusata sosai da lamarin, inda rigimar ta ƙare a wajen.”

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Dakta Ajaka ya ce an zarge shi ne da riƙe takardar sakamakon zaɓen.

Ya yi bayanin cewa a lokacin da yake ƙoƙarin bayyana kansa, ’yan daban sun auka masa inda suka yi masa mugun duka.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like