Connect with us

Kungiyoyi

Hada Kan Manoma Da Makiyaya:  Kungiyar AFAN Reshen Jihar Jigawa Ta Ciri Tuta

Published

on



  • JABIRU A HASSAN, Daga Kano.

    Babu shakka, kungiyar manoma ta kasa reshen jihar Jigawa watau (AFAN) ta ciri tuta wajen kokarin da take yi na tabbatar da cewa rikice-rikice da rashin zaman lafiya tsakanin manoma da makiyaya bai yi tasiri ba a fadin jihar musamman ganin yadda kungiyar take aiki dare da rana wajen dakile duk wani yunkuro na fadace-fadace tsakanin bangarorin biyu.

    Wakilin mu wanda ya sami ziyartar jihar ta Jigawa ya duba yadda kungiyar ta  AFAN a jihar bisa shugabancin Alhaji Idris Yau Mai Unguwa take aikin tabbatar da cewa dukkanin wani yunkuri na  rikicin manoma da makiyaya an dakile shi cikin nasara  da sanin ya kamata, sannan kungiyar tana bakin  kokarin ta  wajen kawo sulhu da hadin kai tsakanin bangarorin biyu.

    Haka kuma a dukkanin garuruwa da kauyuka da wakilin namu ya ziyarta, ya gano cewa rikicin manoma da makiyaya baya tasiri a jihar ta Jigawa saboda kokarin da shugabannin kungiyar ta AFAN keyi dare da rana don tabbatar da ganin ana ci gaba da zaman lafiya da kwanciyar hankali tsakanin manoman jihar da kuma makiyaya a kowane lungu da sako.

    A garin gidan Lage, yankin Karamar hukumar Ringim, wani manomi mai suna Malam Dan Larai ya shaidawa Albishir cewa ” a matsayi na na manomi a wannan yanki, ina na gamsu da yadda  shugabannin mu na AFAN bisa jagorancin Alhaji Idris Yau Mai Unguwa  suke yi wajen ganin ba’a  samun munanan rikice-rikice tsakanin mu da makiyaya ba, kuma wannan ya taimaka wajen samun zaman lafiya da hadin Kai da kuma mutunta juna a wannan yanki namu”.

    Haka kuma a  Karamar hukumar Kafin Hausa wakilin mu ya gana da wani makiyin shanu mai suna Adamu Gide inda ya bayyana cewa suna samun fadakarwa daga kungiyar manoma cewa kada su shiga guraren da amfanin gona yake. Sannan ya nunar da cewa fadan manoma da makiyaya a jihar Jigawa yayi sauki saboda kokarin da kungiyoyin su keyi na tabbatar da cewa ana zaman lafiya.

    Bugu da karai, a garin ganuwar kuka, yankin Karamar hukumar Auyo, wakilin mu ya zanta da Malam Musa Idris manomi Kuma makiyayi wanda ya bayyana cewa a matsayin sa na manomi kuma makiyayi, ya gamsu bisa yadda kungiyar AFAN reshen jihar ta Jigawa take kokarin wayar masu dakai dangane da illolin fadace-fadace tsakanin manoma da makiyaya.

    Bisa wadannan abubuwa da hujjoji da  manoma da makiyaya suka bayyana, kungiyar manoma ta AFAN reshen  jihar Jigawa ta kasance abar misali duk da cewa a baya an dan yi fadace-fadace tsakanin bangarorin biyu har an Sami asarr rayuka da dukiyoyi, amma dai kungiyar ta taka mujimmiyar rawa dangane da zaman lafiya da aka samu.

    Da yake nasa tsokacin, Shugaban kungiyar manoma ta AFAN reshen jihar Jigawa, Alhaji Idris Yau Mai Unguwa ya bayyana cewa ” babu shakka muna Kokari wajen dakile dukkanin wani abu da ya taso Wanda ya shafi rikici tsakanin manoma da makiyaya a wannan jiha ta Jigawa, sannan muna Kokari sosai wajen fadakar da manoma da su kasance masu hakuri da bin dokoki wanda hakan ya taimaka Kwarai wajen samun nasarar magance wadannan rikice-rikice da ake samu”. 

    Sannan ya nunar da cewa gwamnatin jihar Jigawa bisa jagorancin gwamna Muhammad Badaru Abubakar tana yin dukkanin abubuwan da suka kamata wajen tabbatar da cewa kowane bangare na manoma da makiyaya suna samun kulawa ta musamman, don haka muke Kara jinjinawa maigirma gwamna saboda yadda muke samun wannan kulawa a gwamnatance.

    A karshe, Idris Yau Mai Unguwa ya Yi amfani da wannan dama inda ya Yi Kira na musamman ga manoman jihar ta Jigawa da kuma makiyaya da su ci gaba da zama lafiya domin kowa youana bukatar hadin Kai daga kowane bangare a matsayin masu sana’ar noma da kiwo, sannan ya yabawa sauran mataimakan sa na matakin jiha da kananan hukumomi saboda hada hannu da aka yi ana aiki tare.
  • Reply
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Kungiyoyi

Ƙungiyoyin musulunci sun raba wa marayu 900 abinci kyauta a Katsina (Hotuna)

Published

on

Daga Abbas Bamalli

A wani biki mai ƙayatarwa da aka gudanar a gidan marayu na Katsina, sama da marayu 900 ne suka sami farin ciki matuƙa a lokacin da suka samu liyafar cin abincin rana, wanda ƙungiyoyi masu zaman kansu na Musulunci na ƙasa da ƙasa suka yi shirya.

Amir Sultana daga ƙasar Turkiyya tare da haɗin gwiwar Munazzama Da’awa Al-Islam (MADA) daga ƙasar Sudan ne suka shirya taron tare da haɗin gwiwar ofishin uwargidan gwamnan jihar Katsina, Hajiya Zulaihat Raɗɗa.

Shugaban ƙungiyoyi masu zaman kansu, Mufti Ahmed, ya bayyana cewa kimanin marayu 700 a ƙaramar hukumar Katsina da 200 a Jibiya ne suka ci gajiyar wannan kyakkyawan shiri.

Ahmed ya jaddada cewa manufarsu ita ce sanya murmushi a fuskokin marasa galihu, musamman marayu, da ke nuna irin yadda ƙungiyoyin ke gudanar da ayyukan jin ƙai.

KU KUMA KARANTA: Zulum ya raba wa iyalai dubu 40 tallafin abinci da kuɗi a Konduga

An samo kuɗaɗe don shirin ne ta hanyar gudumawa daga mawadata da ɗaiɗaikun mutane da suka amince da ƙungiyoyi masu zaman kansu.

Mufti Ahmed ya bayyana cewa, “Ta hanyar tallafin mun gina rijiyoyin burtsatse kusan 36 a wurare daban-daban a jihar.”

Ya ci gaba da cewa, “Yana daga cikin shirinmu na yin amfani da ragowar kuɗaɗen wajen sanya murmushi a fuskokin marasa galihu, musamman marayu a cikin al’ummarmu.

Wani ɓangare na ayyukanmu shi ne rarraba Alƙur’ani mai girma da kuma bayar da tallafin kuɗi ga marasa galihu.” Baya ga cin abincin rana, ƙungiyoyin sun kuma bayar da gudummawar dalar Amurka 400 ga marayun, wanda hakan ya ƙara haɓaka tasirin ayyukansu na alheri.

Alhaji Isah Muhammad-Musa, kwamishinan ayyuka na musamman, ya yaba da wannan mataki na ƙungiyoyi masu zaman kansu, inda ya ce hakan ya ƙarawa ƙoƙarin Gwamna Dikko wajen tallafawa marasa galihu da marayu a jihar.

Ya bayyana cewa, uwargidan gwamnan ta shirya yin irin wannan aikin na jin ƙai nan ba da jimawa ba, tare da ƙara azama wajen ɗaukaka masu buƙata a cikin al’umma.

Kalli hotona a nan:

Continue Reading

Kungiyoyi

Za a yi taron ƙasashen Musulmai da na Larabawa a Saudiyya kan yaƙin Gaza

Published

on

Saudiyya ta ce za ta karɓi baƙunci taron ƙungiyar Haɗin Kan Ƙasashen Musulmai don tattauna yaƙin Gaza

Ministan zuba jari na ƙasar Saudiyya ya ce, nan da kwanaki masu zuwa ƙasar za ta karɓi baƙuncin taron koli na ƙasashen Larabawa da ƙasashen Musulmai domin tattaunawa kan yaƙin Isra’ila da Falasɗinu.

“Za mu gani a cikin ‘yan kwanaki masu zuwa, Saudiyya ta ƙira wani taron gaggawa na Larabawa a Riyadh,” in ji ministan zuba jari na Saudiyya Khalid Al-Falih, a taron Bloomberg New Economy Forum a Singapore.

KU KUMA KARANTA: An harba rokoki daga Gaza zuwa Tel Aviv

“A cikin kankanin lokaci, makasudin gabatar da waɗannan tarukan guda uku da sauran tarukan ƙarƙashin jagorancin Saudiyya shi ne a kai ga warware rikicin cikin lumana.”

Kamfanin dillancin labaran Etemad ya rawaito cewa, shugaban ƙasar Iran Ibrahim Raisi zai tafi Saudiyya a ranar Lahadi mai zuwa don halartar taron kolin Ƙungiyar Haɗin kan Ƙasashen Musulmai, wadda ita ce ziyarar farko da wani shugaban ƙasar Iran ya kai tun bayan Tehran da Riyadh suka kawo ƙarshen rashin jituwar da aka shafe tsawon shekaru ana yi ƙarƙashin wata yarjejeniya da China ta kulla a watan Maris.

Continue Reading

Jan hankali

Sun yi wa likita dukan kawo wuƙa saboda ‘yar uwarsu ta rasu a Asibiti

Published

on

A ranar Talata ne wani mutum da ɗansa suka fusata inda suka sauke fishin su akan wani babban likita da ma’aikaciyar jinya a cibiyar kiwon lafiya ta tarayya da ke Idi-Aba, Abeokuta bayan da ‘yar uwansu ya rasu a cibiyar.

Rikicin ya ɓarke ne da misalin ƙarfe 2:00 na safiyar ranar Talata, a sashen bayar da agajin gaggawa na asibitin jim kaɗan bayan wata mara lafiya mai shekaru 53 ta rasu.

Shugaban ƙungiyar likitocin Najeriya reshen jihar Ogun, Dakta Kunle Ashimi yayin da yake zantawa da manema labarai, ya yi Allah wadai da harin da ‘yan uwan mamaciyar suka kai wa biyu daga cikin ma’aikatan jinya,akan mutuwar matar a sakamakon ciwon zuciya.

KU KUMA KARANTA:Lauya ya yi wa tsohon mijin wacce yake karewa duka a kotu

Ashimi ya ce Dr Pelumi Somorin likitan ne wanda abin ya shafa,yayin da ba a tantance ko waye ma’aikaciyar jinya ba.

Ya bayyana cewa mahaifin da ɗan, sun mari likitan yayin da aka sanar da su mutuwar yar uwar su.

A cewar Ashimi, matar ‘yar shekara 53 da aka kawo asibitin da ciwon zuciya mai tsanani, wanda ita kanta bayan binciken da ta kawo daga cibiyar da aka turo ta, ya nuna cewa,ba za ta ɗauki fiye da kwana ɗaya ba, sai dai wani ikon Allah.

“Watau ta kasance a matakin ƙarshe na gazawar zuciyarta. An bayyana hakan ga ’yan uwan ta, lokacin da aka kawo ta wurin, amma duk da haka mun yi imanin cewa,Allah kan iya yin wani abu, kuma muna jin cewa ya kamata mu yi iya ƙoƙarinmu don ganin mun taimaka mata.

“Ya taɓa faruwa a baya cewa, wani mutum da ke cikin irin wannan yanayin ya samu sauki tare da kulawar da ta dace.

“Amma abin takaici, wannan majinyaciyar ta mutu da misalin karfe 2 na safe kuma mijin da ɗan marigayiyar suka faɗa kan likitan da ke kula da mara lafiyar lokacin da aka sanar da labarin rasuwarta.

“Sun mari likitan , daga baya kuma suka hau matar mutanen da ke kusa da su suka yi ta jibgarta.

“Waɗannan mutanen kuma sun ci mutuncin wata ma’aikaciyar jinya” in ji shi.

Shugaban ƙungiyar ya ce an sanar da ‘yan sanda game da lamarin, inda ya ƙara da cewa duk da kasancewar ‘yan sanda a wajen,ɗan ya ci gaba da cin mutuncin su.

“An kira ‘yan sanda kuma DPO na ofishin ‘yan sanda na Kempta ya jagoranci tawagar ‘yan sanda zuwa wurin.

“Duk da kasancewar ‘yan sanda, ɗan mamacin ,ya afkawa wata ma’aikaciyar jinya kuma duk ƙoƙarin kwantar da hankalinsa da aka yi, ya ci tura.

“A karshe an kai mutanen biyu zuwa ofishin ‘yan sanda na Kemta, inda aka ɗauki bayanansu da na likitan da aka kai wa harin, ma’aikacin jinya da kuma shaidun da ke kewaye.”

Shugaban na NMA, ya gargadi ‘yan Najeriya da su daina cin zarafin ma’aikatan kiwon lafiya, yana mai shan alwashin cewa, duk wanda aka samu da laifi za a gurfanar da shi a gaban kotu.

“Mun yanke shawarar cewa wannan zai zama na ƙarshe kuma ba za mu yadda a bamu haƙuri ba, mun yanke shawarar mika ƙarar zuwa kotu kuma gobe za mu kasance a kotu.

“An fara duk wata shari’a kuma za mu kai wannan ƙara kotu.

“Muna so mu yi kira da kuma gargaɗi ga duk waɗanda suke zuwa asibitoci a Ogun cewa ƙungiyar likitocin Najeriya, da sauran abokanta da kowane likita, ba za su amince da kalmar “ayi hakuri” nan ba daga yanzu, daga duk wanda ya zagi wani daga cikin membobinmu.

“Za mu yi iya bakin kokarinmu wajen gurfanar da irin waɗannan mutanen kuma ba za mu amince da rokon kowa ba komai girman mutum.

“Don haka, muna rokon duk wanda yake da hankali ya yi tunanin zai iya roƙon mu daga baya don faranta ran jama’a. Ba laifinmu bane”.

Ashimi ya jaddada cewa, cin zarafin ma’aikatan lafiya ya zama ruwan dare gama duniya, wanda har yanzu ba a warware shi ba duk da kamfen da aka yi na daƙile barazanar.

Ya ce “a duniya baki daya, wannan batu ne da ke ci gaba da gudana kuma an gudanar da yakin akan hana hakan, da dama a duk faɗin duniya na yakar tashe-tashen hankula da cin zarafi da ake yi wa ma’aikatan lafiya.

“Musamman a cibiyar kiwon lafiya ta tarayya a Abeokuta, jihar Ogun da sauran asibitocin da ke kewayen Jihar Ogun waɗanda ke ƙarkashin ikonmu a matsayin kungiyar likitocin Najeriya.

“Mun gudanar da yaƙi da hani,da irin halayyar nan, da dama a kan wannan taron a baya kuma bayan yawan rokon da muka yi, sai da muka roƙi likitocinmu da su karɓi uzurin waɗanda suke yin abun

“Abubuwa irin wannan ba sa raguwa, a zahiri, wannan yana faruwa sau da yawa a lokuta da dama.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like