Connect with us

Labari

Gwamnatin Jihar Kaduna Ta Tabbatar Da Kisan Mutane 32, Yayin Da Ta Karyata Zancen Jirgi Mai Saukar Ungulu

Published

on

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

GWAMNATIN Jihar Kaduna ta tabbatar da kisan wasu mutane talatin da biyu (32) a ciki wani sabon harin da wasu yan Bindiga suka kai a cikin yan kwanakin nan a wasu kauyukan da ke karkashin karamar hukumar Kajuru ta Jihar Kaduna, kana ta karyata wani bayanin da ke cewa ‘yan Bindigan sun koma kai hari a wani Jirgi mai saukar Ungulu.

Bayanin hakan na kunshe ne a cikin wata takarar sanarwa da kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida, Samuel Aruwan ya fitar a ranar Alhamis.

Sanarwar ta kara da cewa, “ta samu rahoton farko daga hukumomin tsaro, cewa ‘yan bindiga sun kai hari kauyukan Dogon Noma, Unguwan Sarki da Unguwan Maikori a karamar hukumar Kajuru a ranar Lahadin da ta gabata.”

Rahotanni sun bayyana cewa, ‘yan bindigar sun mamaye yankin a kan babura inda suka yi ta lalata gidaje da dama, yayin da suka kai hari tare da kashe wasu mutanen yankin.

Acewarta, tun bayan harin da aka kai a ranar lahadi, hukumomin tsaro da shugabannin gargajiya da ke wuraren ke ta kokarin tattara bayanai game da ci gaban da ake samu kana suke sanar da Gwamnatin.

Sanarwar ta ce, ya zuwa lokacin wannan rahoto, an tabbatar da mutuwar mutane 32 bayan harin.

Yayin da Gwamnati ke jimamin kisan gilla da kona gidaje da aka yi a wuraren da aka kai harin, an buga wani rahoto da ke nuni da cewa ‘yan ta’adda sun kashe wadanda harin ya rutsa da su ta hanyar amfani da jirgin sama mai saukar ungulu.

Gwamnatin Jihar Kaduna na son yin karin haske kan rahotannin da aka samu tun ranar Lahadi, inda ta ce ‘Yan bindigar sun kai hari a wurare biyu a yankin, na farko inda suka kashe mutane 31 a yankin, kana daga nan suka nufi Ungwan Maikori, inda suka kashe mutum daya tare da kona wasu gidaje.

“Tun da farko, wani jirgin sama mai saukar ungulu (a karkashin Operation Whirl Punch) ya kai shawagi na agaji a yankin inda ya leka wurare biyu, kuma wuri na farko, ya kuma hango kone-konen gidaje da kadarori.

“Jirgin sama mai saukar ungulu ya tare ‘yan bindigar a wasu wurare yayin da a wuri na karshe (Ungwan Maikori) ya samu nasarar tare su har da kama su yayin da suke kokarin tsere wa, kafin isowar sojojin kasa izuwa yankin gaba daya don kai agaji.

Ta ce “Isowar dakarorin jirgin ne ya hana ‘yan bindigar ci gaba da kai hare-hare kan ‘yan kauyen bayan ‘yan bindigar sun kashe wani dan unguwar tare da kona gidaje da dama.

“Labarin cewa wani jirgin sama mai saukar ungulu ya bayar da tallafin sama ga ‘yan bindigar kan mutanen yankin, wannan labarin ba gaskiya ba ne, don haka magana ce mara tushe.

“Gwamnatin jihar Kaduna da ta bi diddigin al’amura, ta ga abin takaicin yadda wani sashe na kafafen yada labarai ke yada wani rahoto da ba a tabbatar da shi ba, ba tare da la’akari da tasirinsa kan tsaro, doka da oda ba.

“An gayyaci shaidun gani da ido kan rahoton wani jirgin sama mai saukar ungulu da ke taimaka wa ‘yan bindiga da ke kashe mutanen da ba su ji ba ba su gani ba, da su gabatar da bayanan ga gwamnati bisa goyon bayan hujjojin da ba za a iya tantancewa ba.

“Sojoji, ’yan sanda da sauran hukumomin da ke aiki a yankin gaba daya sun cancanci yabo da kwarin gwiwa ne, maimakon rage musu kwarin gwiwa.

“A cikin sa’o’i 72 da suka gabata, jami’an tsaro sun gudanar da wani gagarumin farmaki a yankin gaba daya, kuma suna kan bin wani fitaccen dan ta’adda da ya jikkata.

“Hakazalika, wasu da dama da aka yi garkuwa da su, ciki har da wani dan kasar waje da aka yi garkuwa da su a wani wurin hakar ma’adinai, an kubutar da su bayan mumunar hulda da ‘yan fashi.

“Gwamna Nasir El-Rufa’i da ya samu rahoton harin, ya nuna matukar bakin ciki tare da addu’ar Allah ya jikan wadanda lamarin ya shafa. Ya kuma mika sakon ta’aziyyarsa ga iyalan wadanda lamarin ya shafa,” in ji sanarwar.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Jirgin sama ya yi saukar gaggawa a Legas | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like