Gobara
Gobara ta tashi a hukumar shari’ar jihar Kano
![](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2023/11/Screenshot_20231122-084249_1.jpg)
Gobara ta tashi a hukumar shari’a ta jihar Kano inda ta ƙone wani ɓangare kurmus.
Aminiya ta rawaito cewa duka ofisoshin da ke ɓangaren da gobarar ta tashi sun ƙone kurmus, kuma har kawo yanzu ba a san dalilin tashinta ba.
Tashi gobarar a ranar talata ya tsayar da ayyukan hukumar cak.
Wani Ganau da ke aiki a hukumar ya shaidawa Aminiya cewa suna zaune suka hango hayaki na tashi daga wani ɓangare na hukumar.
“Mun idar da sallah ke nan sai muka hango hayaki na tashi daga cikin hukumar.
“Kafin mu san abin yi har motar hukumar kashe gobara ta shigo harabar hukumar inda suka shiga aiki,” in ji shi.
Batulu Isah Waziri, muƙaddashiyar Darakta-Janar na hukumar ta bayyana cewa tana ofishinta aka sanar da ita tashin gobarar inda ta je ta ga yadda gobarar ta lahanta ofisoshin daraktocin Hukumar da wasu kayayyaki.
KU KUMA KARANTA: Gobara ta tashi a kasuwar Gamboru da ke Maiduguri
“Lokacin da na je wurin gobarar tana kan ci, na ga yadda ta lahanta ofisoshin daraktocinmu guda biyu da wasu ofisoshi na ma’aikatansu wanda kuma kayayyakin aikinsu da suka haɗa da tebura da kujeru da takardu duk sun ƙone kurmus,” in ji ta.
Kakakin Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano, Saminu Yusuf Abdullahi ya ce da zarar hukumarsu ta kammala haɗa bayanai game da dalilin tashin gobarar da kuma girman asarar da ta yi za su sanar da manema labarai.
Boko Haram
An tabbatar da mutuwar masu juna biyu a cikin harin da aka kai a Borno
![An tabbatar da mutuwar masu juna biyu a cikin harin da aka kai a Borno](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/06/IMG_9718.jpeg)
An tabbatar da mutuwar masu juna biyu a cikin harin da aka kai a Borno
An kasha aƙalla mutane 18, yayin da wasu 30 suka jikkata bayan wasu jerin hare-haren da ake zargin wasu mata ‘yan ƙunar baƙin wake ne suka kai a jihar Borno a jiya Asabar, in ji shugaban hukumar bayar da agajin gaggawa ta yankin.
Borno dai na cikin shekaru 15 na hare-haren masu iƙirarin kishin Islama wanda ya yi sanadiyar mutuwar dubban mutane tare da raba wasu miliyoyi da humallan su.
Duk da cewa sojojin Najeriya sun rage ƙarfin mayaƙan, amma har yanzu suna kai munanan hare-hare kan fararen hula da kuma wuraren tsaro.
KU KUMA KARANTA:Gobara ta tashi a matatar man Ɗangote
Barkindo Saidu, shine babban Daraktan Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Borno, ya ce wasu da ake zargin ‘yan ƙunar baƙin wake ne suka kai hari daban-daban a wajen bikin aure da jana’iza da kuma asibiti, inda suka kashe mutane tare da jikkata wasu da dama a garin Gwoza.
Saidu ya ce an tabbatar da mutuwar mutum 18, adadin da ya haɗa da ƙananan yara da manya da ma mata masu juna biyu.
Sai dai babu wata ƙungiyar ko wani mutun da ya ɗauki alhakin kai wannan harin.
Boko Haram da ISWAP da ta ɓalle kanta, su ne ƙungiyoyin ‘yan bindiga da suka fi yawan gudanar da ayyukan su a jihar Borno, wani babban yanki na karkara mai girman gaske.
Gobara
Tinubu ya jajantawa mutanen da gobarar kasuwar Karu ta shafa
![Tinubu ya jajantawa mutanen da gobarar kasuwar Karu ta shafa](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/06/IMG_9713.png)
Tinubu ya jajantawa mutanen da gobarar kasuwar Karu ta shafa
Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya miƙa saƙon jajensa ga ‘yan kasuwar da shaguna da dukiyoyinsu suka ƙone a gobarar da ta tashi a kasuwar Karu a daren Alhamis.
Sanarwar da hadimin shugaban ƙasar akan harkokin yaɗa labarai, Ajuri Ngilale ya fitar a ranar Juma’a ta ce, shugaban ƙasar ya yi takaicin samun labarin gobarar da ta shafi wani sashe na kasuwar.
Da yammacin ranar Alhamis, gobara ta laƙume wani yanki na kasuwar, inda ta lalata ɗimbim dukiya da sauran kayayyaki masu daraja.
KU KUMA KARANTA:Gobara ta tashi a matatar man Ɗangote
Sanarwar ta ƙara da cewar, shugaban ƙasa na miƙa saƙon jajensa ga ilahirin ‘yan kasuwar da wannan mummunan al’amari ya shafa, sannan yana ba su tabbacin samun tallafi daga gwamnatinsa.
Shugaban ƙasar ya kuma yi ƙira da a riƙa taka tsantsan da ɗaukar matakan kariya, domin kare afkuwar gobara da sauran bala’o’i a nan gaba.
Gobara
Gobara ta tashi a matatar man Ɗangote
![Gobara ta tashi a matatar man Ɗangote](https://neptuneprimehausa.com/wp-content/uploads/2024/06/Dangote-1-750x430-1.jpg)
Gobara ta tashi a matatar man Ɗangote
Gobara ta tashi da yammacin yau a wani sashe na matatar man Ɗangote da ke kusa da Lekki a Legas.
Jami’an agajin gaggawa sun ɗauki matakin shawo kan lamarin, kuma a cewar rahotannin farko, ba a samu raunuka ba.
Kawo yanzu dai ba a san musabbabin tashin gobarar ba, kuma ana ci gaba da gudanar da bincike don gano girman barnar da aka yi da kuma abin da ya haddasa faruwar lamarin.
Da take mayar da martani kan gobarar a cikin wata sanarwa da Ɗangote ya fitar, mai ɗauke da sa hannun Anthony Chiejina, ƙungiyar ta ce, “Mun yi gaggawar shawo kan wata ‘yar karamar gobara a masana’antar sarrafa iska (ETP), a yau Laraba 26 ga watan Yuni.
KU KUMA KARANTA: Gobara ta kashe jarirai shida a Indiya
“Babu wani dalili na tashin hankali yayin da matatar ta ke aiki kuma babu wani rauni da aka samu ko lahani ga dukkan ma’aikatanmu da ke bakin aiki.”
Matatar dangote wani katafaren aiki ne da ake ginawa wanda ake hasashen zai iya tace ganga 650,000 a kowace rana.
-
Kotu1 year ago
Kotu tayi watsi da ƙarar APC game da zaɓen Abba Gida Gida
-
Labarai10 months ago
Dalilin da ya sa na saka wa matata sasari – Wani magidanci a Potiskum
-
Ƙasashen Waje1 year ago
Ɗaliban Najeriya a Sudan sun nemi a kwaso su daga ƙasar
-
Labarai1 year ago
‘Yan banga sun kama wani mutum da ke yunƙurin sace yarinya a Kano