Connect with us

Gobara

Gobara a cibiyar sayar da gas a Kenya, ta kashe mutum 2 da jikkata fiye da 300

Published

on

An samu gagarumar fashewar a wata cibiyar sayar da gas na girki a Nairobi, babban birnin Kenya inda aƙalla mutum biyu suka mutu kuma mutum 300 suka jikkata, kamar yadda ƙungiyar bayar da agaji ta Red Cross ta Kenya da kuma jami’ai suka bayyana.

Lamarin ya faru ne ranar Alhamis da daddare, a cewar ganau. Ana fargabar cewa za a iya samun ƙarin mace-mace.

“Ma’aikatan bayar da agajin gaggawa daban-daban sun ƙuɓutar da mutum 271 inda aka kai su cibiyoyoin kiwon lafiya da ke Nairobi,” kamar yadda ƙungiyar ba da agaji ta Red Cross a Kenya ta bayyana ranar Juma’a a shafinta na X.

KU KUMA KARANTA: Tashin gobara a kasuwar waya a Damaturu, an yi asarar dukiya mai yawa

Ta ƙara da cewa an yi wa mutum 27 magani nan-take a wurin da lamarin ya faru.

Bidiyoyin da aka dauka a unguwar Embakasi sun nuna ‘yan kwana-kwana suna kokarin kashe gobarar.

Wani mai magana da yawun gwamnati ya bayyana cewa ana kokarin cika tukwanen iskar gas ne a lokacin da gobarar ta tashi da misalin karfe sha biyu na dare ranar Alhamis.

Ganau sun bayyana wa kafafen watsa labarai na kasar cewa sun ji mostin kasa bayan fashewar.

Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Boko Haram

An tabbatar da mutuwar masu juna biyu a cikin harin da aka kai a Borno

Published

on

An tabbatar da mutuwar masu juna biyu a cikin harin da aka kai a Borno

An tabbatar da mutuwar masu juna biyu a cikin harin da aka kai a Borno

An kasha aƙalla mutane 18, yayin da wasu 30 suka jikkata bayan wasu jerin hare-haren da ake zargin wasu mata ‘yan ƙunar baƙin wake ne suka kai a jihar Borno a jiya Asabar, in ji shugaban hukumar bayar da agajin gaggawa ta yankin.

Borno dai na cikin shekaru 15 na hare-haren masu iƙirarin kishin Islama wanda ya yi sanadiyar mutuwar dubban mutane tare da raba wasu miliyoyi da humallan su.

Duk da cewa sojojin Najeriya sun rage ƙarfin mayaƙan, amma har yanzu suna kai munanan hare-hare kan fararen hula da kuma wuraren tsaro.

KU KUMA KARANTA:Gobara ta tashi a matatar man Ɗangote

Barkindo Saidu, shine babban Daraktan Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Borno, ya ce wasu da ake zargin ‘yan ƙunar baƙin wake ne suka kai hari daban-daban a wajen bikin aure da jana’iza da kuma asibiti, inda suka kashe mutane tare da jikkata wasu da dama a garin Gwoza.

Saidu ya ce an tabbatar da mutuwar mutum 18, adadin da ya haɗa da ƙananan yara da manya da ma mata masu juna biyu.

Sai dai babu wata ƙungiyar ko wani mutun da ya ɗauki alhakin kai wannan harin.

Boko Haram da ISWAP da ta ɓalle kanta, su ne ƙungiyoyin ‘yan bindiga da suka fi yawan gudanar da ayyukan su a jihar Borno, wani babban yanki na karkara mai girman gaske.

Continue Reading

Gobara

Tinubu ya jajantawa mutanen da gobarar kasuwar Karu ta shafa

Published

on

Tinubu ya jajantawa mutanen da gobarar kasuwar Karu ta shafa

Tinubu ya jajantawa mutanen da gobarar kasuwar Karu ta shafa

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya miƙa saƙon jajensa ga ‘yan kasuwar da shaguna da dukiyoyinsu suka ƙone a gobarar da ta tashi a kasuwar Karu a daren Alhamis.

Sanarwar da hadimin shugaban ƙasar akan harkokin yaɗa labarai, Ajuri Ngilale ya fitar a ranar Juma’a ta ce, shugaban ƙasar ya yi takaicin samun labarin gobarar da ta shafi wani sashe na kasuwar.

Da yammacin ranar Alhamis, gobara ta laƙume wani yanki na kasuwar, inda ta lalata ɗimbim dukiya da sauran kayayyaki masu daraja.

KU KUMA KARANTA:Gobara ta tashi a matatar man Ɗangote

Sanarwar ta ƙara da cewar, shugaban ƙasa na miƙa saƙon jajensa ga ilahirin ‘yan kasuwar da wannan mummunan al’amari ya shafa, sannan yana ba su tabbacin samun tallafi daga gwamnatinsa.

Shugaban ƙasar ya kuma yi ƙira da a riƙa taka tsantsan da ɗaukar matakan kariya, domin kare afkuwar gobara da sauran bala’o’i a nan gaba.

Continue Reading

Gobara

Gobara ta tashi a matatar man Ɗangote

Published

on

Gobara ta tashi a matatar man Ɗangote

Gobara ta tashi a matatar man Ɗangote

Gobara ta tashi da yammacin yau a wani sashe na matatar man Ɗangote da ke kusa da Lekki a Legas.

Jami’an agajin gaggawa sun ɗauki matakin shawo kan lamarin, kuma a cewar rahotannin farko, ba a samu raunuka ba.

Kawo yanzu dai ba a san musabbabin tashin gobarar ba, kuma ana ci gaba da gudanar da bincike don gano girman barnar da aka yi da kuma abin da ya haddasa faruwar lamarin.

Da take mayar da martani kan gobarar a cikin wata sanarwa da Ɗangote ya fitar, mai ɗauke da sa hannun Anthony Chiejina, ƙungiyar ta ce, “Mun yi gaggawar shawo kan wata ‘yar karamar gobara a masana’antar sarrafa iska (ETP), a yau Laraba 26 ga watan Yuni.

KU KUMA KARANTA: Gobara ta kashe jarirai shida a Indiya

“Babu wani dalili na tashin hankali yayin da matatar ta ke aiki kuma babu wani rauni da aka samu ko lahani ga dukkan ma’aikatanmu da ke bakin aiki.”

Matatar dangote wani katafaren aiki ne da ake ginawa wanda ake hasashen zai iya tace ganga 650,000 a kowace rana.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like