Connect with us

Labari

Gamayyar Kungiyoyin Ma’aikatan Masakun Kaduna Sun Koka Kan Rashin Biyan Hakkokinsu

Published

on

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

GAMAYYAR kungiyar ma’aikatan Masaku da aka kulle ba tare da biyansu hakkinsu ba a jihar Kaduna, sun yi kira ga Gwamnatin Tarayya da Gwamnatin Jihar Kaduna da su gaggauta kawo musu dauki ta hanyar biyansu hakkokinsu da ba a biya su ba domin samun ingantacciyar rayuwa ga ‘ya’yansu.

Da suke jawabi yayin wani taron zanga-zangar lumana da aka shirya a harabar Kaduna Textiles Limited (KTL) a ranar Alhamis, ma’aikatan sun nuna damuwarsu kan shiru da suka dade su nani wanda yake kashe su a kullum tun bayan rufe masana’antar sama da shekaru 20 da suka gabata.

A cewar shugaban gamayyar, Kwamared Jeibe Wordam Simdik, ya bayyana cewa aikin masaku a Kaduna da wasu sassan Najeriya sun bayar da gudunmawa sosai wajen habaka tattalin arzikin kasa.

Ya kara da cewa, tun bayan rufe wadannan masana’antun da aka rufe, sun fuskanci munanan kalubale da suka hada da rashin lafiya, tabarbarewar ilimin ’ya’yansu, lalacewar aure, matansu da ‘ya’yansu sun zama mabarata ta hanyar barace-barace domin ciyar da su.

“Ma’aikatanmu sun zama abokan cinikin kotun saboda rashin biyan kudin haya.
Bisa la’akari da abubuwan da ke faruwa, da yawa daga cikin ma’aikatanmu da danginmu suna mutuwa cikin takaici saboda haka, muna kira ga duk masu ruwa da tsaki a Najeriya da su jikanmu tare da yin adalci a cikin halin da muke ciki.”

“Sake bude duk wasu masakun da aka rufe a Najeriya da suka hada da Kaduna Textiles Limited, Arewa Textiles PLC, NORTEX Nigeria Limited, da FINETEX Limited, zai samar da damar aiki ga hadakar matasa da kuma rigakafin rashin tsaro a Najeriya.” Ya Jaddada

“Shugabanninmu na yanzu da suka jagorance mu sama da shekaru 20, wani abun dogaro suka bar wa ‘ya’yanmu, saboda kin biyan mu hakkinmu bayan sun yi shekaru da dama suna hidima.” Inji Comrade Jeibe

A cewarsa, shugaban kasa Muhammad Buhari ya yi mana alkawarin cewa duk masana’antun za a farfado da su amma an yi watsi da mu. Hakazalika Gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasir El-Rufa’i ya yi alkawarin farfado da rufaffun masaku a lokacin yakin neman zabensa a shekarar 2015 da 2019, amma duk an watsar.

“Muna kira ga shugaban kasa Muhammadu Buhari, shugaban kungiyar gwamnonin Arewa kuma shugabanin majalisar wakilai ta kasa da su tausaya tare da yin adalci su biyamu hakkinmu.”

“Muna kira ga masu wannan masana’antar da aka rufe da su biya mana bukatunmu domin muna son iyalanmu su kasance cikin rayuwa mai kyau kamar sauran al’ummar Najeriya.” Ya koka

A karshe, mambobin kungiyar da ke karkashin inuwar gamayyar kungiyar sun yi alkawarin cewa daukacin ma’aikatan da ke aikin masaku sun sha alwashin yin amfani da katin zabensu wato P.V.C wajen zaben 2023 ga wadanda za su yi la’akari da halin da suke ciki yanzu don kawo musu dauki.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like