Connect with us

Siyasa

Gamayyar Al’ummar Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Dauki Dogara A Matsayin Abokin Takarar Shi

Published

on

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

WATA gamayyar Kungiyoyin al’ummar Arewa da ke fafutukar tabbatar da zaman lafiya da ci gaba (CFPP), sun buƙaci dan takarar Kujerar Shugaban Kasa, a karkashin Jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu da ya dauki tsohon kakakin Majalisar Wakilai na Tarayya, Honarabul Yakubu Dogara a matsayin abokin takarar shi na zabe mai zuwa a shekarar 2023.

Gamayyar Kungiyoyin wanda a ranar Asabar suka gudanar da wani taron manema labarai a sakatariyar Kungiyar Yan Jaridu ta Najeriya (NUJ), reshen Jihar Kaduna, sun bayyana goyon bayan su ga tsohon dan Majalisar wanda su ka kuma bayyana shi a matsayin wanda ya fi kowa cancantar zama a matsayin mataimakin Shugaban Kasa ga dan takarar Jam’iyyar ta APC.

Da yake jawabi a wajen taron a madadin sauran al’ummar, Shugaban gamayyar Kungiyoyin ta (CFPP), Dakta Muhammad Chindo, ya jaddada bukatar su na cewa dole ne mataimakin dan takarar Kujerar shugabancin Kasar a karkashin jam’iyyar ta APC ya zama Kirista ne, kuma shi Honarabul Dogara ne wannan mutumin.

Gamayyar Kungiyoyin, wadanda tare da magoya bayansu akalla sama da mutane 70 wadanda suka hada da maza da mata da suka halarci wannan taron, sun zabi goyon bayan tsohon kakakin majalisar wakilai ta tarayya Rt. Hon. Yakubu Dogara ne a matsayin Kiristan da ya fi kowanne dacewa.

Kodinetan kungiyar na kasa, Dokta Muhaamad Chindo, ya kara da cewa mataimakin shugaban kasa na gaba, ya nunar da cewa dole ne mataimakin ya zama kirista wanda ya zarce ra’ayin kowa a tun farko wanda rashin yin hakan na da nasabar kawo rudani a cikin addini da sharri na kabilanci da bangaranci.

Gamayyar ta kuma bayyana cewa, a bisa la’akari da nau’o’in daban-daban na Najeriya, da kuma bukatar tabbatar da adalci da kasancewarsa mafi dacewa, dole ne wanda za a zaba a matsayin mataimakin shugaban kasa ya kasance wanda yake da halayen da ake bukata da kuma kwarewa a siyasance.

A cewar gamayyar, irin wannan mutumin dole ne ya zama Kirista nagari wanda ya hada kai wajen samar da hadin kaia tsakanin al’ummar kasarmu daban-daban.

Sun kara da cewa, bayan kammala bincike da kwazo, domin ci gaba da jajircewarsu da sadaukarwar da suka yi wajen ganin an tabbatar da dunkulewar Najeriya, gamayyar ta kammala da cewa Rt. Honarabul Dogara shi ne mutumin da yafi cancanta da mukamin mataimakin Shugaban Kasa a karkashin Jam’iyyar ta APC.

A cewarsu zabin Dogara a matsayin wanda ya fi dacewa ya samo asali ne daga wasu dalilai guda biyar da suka zabe shi kuma suka yi magana da shi na tsawon shekaru har sai da radin kansa ya sauka, a matsayinsa na dan siyasa wanda aka gwada kuma aka amince da shi, wanda ya gina gada da amincewar mazabar DASS. /Tafawa Balewa/Bogoro na mutane daban-daban, kana ya gina masallatai ga musulmi fiye da coci da sauransu.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Siyasa

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Published

on

APC ta dakatar da ɗan Majalisa kan cin amana a Zamfara

Jam’iyyar APC reshen Jihar Zamfara ta dakatar da Ɗan Majalisar Wakilai, Aminu Jaji bisa wasu zarge-zargen da ake yi masa na cin amanar jam’iyyar.

Sakataren Yaɗa Labarai na Jam’iyyar APC na Jihar, Malam Yusuf Idris ne ya sanar da dakatarwar a wani taron manema labarai a Gusau a ranar Juma’a.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa, Jaji yana wakiltar mazaɓar Ƙaura-Namoda/Birnin-Magaji a Majalisar Wakilai a ƙarƙashin jam’iyyar APC.

Idris ya ce wasu zarge-zargen da ake yi wa Ɗan Majalisar sun haɗa da aikata rashin gaskiya da rashin zuwa tarurrukan jam’iyyar da kuma sauran ayyuka.

KU KUMA KARANTA: Kotun Najeriya ta bayar da umarnin dakatar da asusun banki fiye da dubu 1

Ya ce, matakin ya biyo bayan sanarwar dakatarwar da aka yi wa Jaji daga shugabannin jam’iyyar APC na mazaɓar Birnin-Magaji bisa zargin cin amanar jam’iyyar da dai sauran abubuwan da suka saɓa wa jam’iyyar.
Idris ya ce, “Kwamitin zartaswa na jam’iyyar APC na ƙaramar hukumar Birnin Magaji ne ya miƙa sanarwar dakatarwar zuwa hedikwatar jam’iyyar APC ta jihar.

Bayanai sun ce kwamitin zartaswar jam’iyyar APC na jihar ya gudanar da taron gaggawa a sakatariyar jam’iyyar da ke Gusau a ranar Juma’a 17 ga watan Mayu, 2024, inda aka gabatar da batun dakatar da Jaji ga ‘yan majalisar zartarwar jihar.

Continue Reading

Labarai

Tsohon gwamnan Katsina, Shema ya sauya sheƙa zuwa APC

Published

on

Tsohon gwamnan jihar Katsina, Ibrahim Shema, a hukumance ya koma jam’iyyar APC Mai mulki a jihar.

Shema, ya kasance gwamnan jihar a tsakanin shekarar 2007 zuwa 2015, a ƙarƙashin jam’iyyar PDP.

Tsohon gwamnan ya yi rajista ne a ofishin jam’iyyar na mazaɓar Shema, ƙaramar hukumar Dutsin-ma, inda shugaban jam’iyyar na jihar, Sani Aliyu-Daura ya ba shi katin zama ɗan jam’iyyar APC.

Lambar katin Shema ta zama ɗan jam’iyyar ita ce: 26551.

KU KUMA KARANTA:Gwamnatin Yobe za ta mayar da kwale-kwalen Dufuna mai shekaru 8,000 zuwa cibiyar yawon buɗe ido

Malam Aliyu-Daura ya yabawa Gwamna Dikko Raɗɗa da kuma tsohon gwamnan jihar Aminu Masari wanda ya gada, a bisa rawar da suka taka wajen ganin Shema ya sauya sheƙa.

Don haka ya tabbatar wa tsohon gwamnan cewa za a yi masa adalci kamar kowane ɗan jam’iyya.

Shugaban ma’aikata na Raɗɗa, Jabiru Abdullahi-Tasuri, shi ne ya miƙa katin zama ɗan jam’iyya ga Shema a madadin gwamnan a jiya Alhamis a Dutsin-ma.

Continue Reading

Labarai

Fusatattun matasa sun lakaɗawa kwamishina duka a wajen zaɓen fidda gwani

Published

on

Banji Ajaka, kwamishinan lafiya na jihar Ondo, ya gamu da fushin matasa a jiya Asabar yayin da ake gudanar da zaɓen fidda gwani na gwamna na jam’iyyar APC mai mulki a jihar.

Daily Trust ta gano cewa Dakta Ajaka, wanda ke Mazaɓar Ugbo 3, a ƙaramar hukumar, ana zarginsa da ɓoye takardar sakamakon zaɓen.

Shaidu sun tabbatar da faruwar lamarin a wata tattaunawa da suka yi da manema labarai, inda suka yi zargin cewa fusatattaun matasan ‘ya’yan jam’iyyar APC ne da ke adawa da tsarin da aka bi wajen gudanar da zaɓen.

Ɗaya daga cikin waɗanda suka shaida lamarin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana cewa rikicin ya faro ne lokacin da ‘yan ɗaya ɓangaren na jam’iyyar suka buƙaci ganin takardar sakamakon zaɓen na fidda gwani.

KU KUMA KARANTA:An yi jana’izar tsohon gwamnan Ondo, Rotimi Akeredolu

“Sun fusata ne suka buƙaci jami’in zaɓe ya ba su takardar sakamakon zaɓen sai kuwa ya ce ta na wajen Ajaka.

“Don haka suka yi masa duka a wurin, inda kuma garinsu ne. Jama’a sun fusata sosai da lamarin, inda rigimar ta ƙare a wajen.”

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Dakta Ajaka ya ce an zarge shi ne da riƙe takardar sakamakon zaɓen.

Ya yi bayanin cewa a lokacin da yake ƙoƙarin bayyana kansa, ’yan daban sun auka masa inda suka yi masa mugun duka.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like