Connect with us

Labarai

Fiye da kashi 70 na waɗanda aka kashe a Najeriya a watan Yuni a Arewa suke

Published

on

Daga Fatima GIMBA, Abuja

Binciken ya ce yunƙurin da gwamnati ta yi na hana satar mutane bai yi nasara ba a watan Yuni sa’o’i 2 da suka wuce.

Wata ƙididdiga game da sha’anin tsaro a Najeriya ta nuna cewa kashi 75.6 na mutanen da aka kashe sakamakon hare-hare a watan Yuni a arewacin ƙasar suke.

Sabuwar ƙididdiga, wadda kamfanin Beacon Consulting Limited da ke nazari kan harkokin tsaro ya fitar a wannan watan, ta bayyana cewa an kai hari 338 a fadin kasar a watan na Yuni lamarin da ya kai ga sace mutum 651.

Kazalika an kashe “mutum 765. Wannan lamari ya faru ne a ƙananan hukumomi 185 da ke jihohi 36 da Abuja, babban birnin kasar.”

Alkaluma kan lamarin sun bayyana cewa kashi 28.6 na kashe-kashen sun faru ne a Arewa maso Gabas ( an kashe mutum 219 ), kashi 23.5 a Arewa ta Tsakiya ( inda aka kashe mutum 180), kashi 23.5 a Arewa maso Yamma (mutum 180 sun mutu).

Kazalika kashi 10.5 na kashe-kashen ya faru ne a Kudu maso Yamma ( an kashe mutum 80), yankin Kudu maso Gabas na da kashi 9.2 (an kashe mutum 70) da kuma Kudu maso Kudu mai kashi 4.7 (an kashe mutum 36).

“Kashi 75.6 na mutanen da aka kashe a watan Yunin 2022 na zaune ne a arewacin Najeriya,” in ji kididdigar.

Ta ƙara da cewa bincike ya nuna cewa galibin mutanen sun mutu ne sakamakon hare-hare da ake kai wa a musamman yankunan karkara – inda aka kashe mutum 350 a watan na Yuni, yayin da musayar wuta tsakanin ‘yan bindiga da jami’an tsaro ta yi sanadin mutuwar mutum 183, sannan kwanton-bauna ya yi sanadin ajalin mutum 79.

Haka kuma bincike ya nuna cewa a watan na Yuni an fi kashe mutanen Borno inda aka kashe mutum163, sai mutum 90 da aka kashe Benue, an kashe mutum 82 a Kaduna, mutum 65 a Neja dsa kuma mutum 42 a Zamfara.

Jihar Ondo ce ke kan gaba a cikin jihohin Kudu maso Yamma da aka yi kisa inda aka kashe mutum 55, yayin da a Kudu maso Gabas an fi kashe mutane a Ebonyi inda mutum 28 suka mutu.

An fi sace mutane a Sokoto

A game da satar mutane kuwa, Jihar Sokoto ke kan gaba da mutum 107. Jihar Kaduna ke biye mata inda aka sace mutum 92, sai Jihar Katsina inda aka sace mutum 90.

Sauran su ne Neja inda aka sace mutum 60, an sace mutum 56 a Zamfara, yayin da aka sace mutum 56 a Abuja, da kuma mutum 47 a Borno.

Rahoton ya ce a watan na Yuni, kokarin gwamnati ya yi matukar rage lamuran rashin tsaro da kashe-kashe sai dai bai rage yawaitar sace-sacen jama’a ba idan aka kwatanta da watan Mayun 2022.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Sarkin Gwandu ya naɗa ɗan Buran ɗin Gwandu babba

Published

on

Sarkin Gwandu ya naɗa ɗan Buran ɗin Gwandu babba

Sarkin Gwandu ya naɗa ɗan Buran ɗin Gwandu babba

Daga Haruna Abdulrashid

Shugaban majalisar sarakuna ta jihar Kebbi, Mai martaba Sarkin Gwandu, Manjo-Janar Muhammadu Ilyasu Bashar Mni, ya karrama Shugaban hukumar jin daɗi da walwalar Alhazzai ta ƙasa, Malam Jalal Muhammad Arabi da sarautar (ƊAN BURAN GWANDU BABBA) inda mai martaba sarki ya aike da tawaga zuwa birnin tarayya Abuja domin gabatar da wannan karramawa zuwa ga Malam Jalal Arabi.

Da ya ke jawabi a madadin mai martaba sarkin Gwandu Alhaji Aminu Ahmad, Sarkin Fadan Gwandu ya bayyana cewa mai martaba sarkin Gwandu ya amince da bayar da wannan karramawa ga Malam Jalal ne a bisa jajircewa da kuma taimako da yake yiwa Alhazzan Najeriya tare da haɗin kai da yake bawa shugabanni a kan abin da ya shafi harkar aikin Hajji mussaman a bana.

Shi ma shugaban hukumar jin daɗin da walwalar Alhazai ta jihar Kebbi, Alhaji Faruƙu Musa Yaro Enabo, Jagaban Gwandu, ya bayyana jin daɗin shi matuƙa a kan wannan karramawar da aka yi wa maigidan shi.

Ya kuma yabawa mai martaba Sarkin Gwandu Manjo-Janar Muhammadu Ilyasu Bashar akan yadda yake gabatar da kyakkyawan jagoranci zuwa ga Al’ummar Gwandu.

Wannan bayar da takardar karramawa ta sarautar (ƊAN BURAN GWANDU) Sun haɗa da Alh Aminu Ahmed Sarkin Fadan Gwandu, Alh Aminu Abubakar Gulumbe Uban ƙasar Gulumbe, Alh. Mustapha Ka’oje Sarkin Bargun Ka’oje, Alh Lamiru Shehu Sakataren Sarakunan jihar Kebbi, Alh Faruƙu Musa Yaro Enabo Jagaban Gwandu, Alh Usman Osho da Alh Rilwanu Awwal.

Mai girma Shugaban hukumar Jin daɗi da walwalar Alhazzai ta jihar Kebbi, Malam Jalal Arabi, ya bayyana jin daɗin shi sosai ganin wanan karramawa da ya samu daga masarautar Gwandu.

Ya kuma ce jihar Kebbi ta zama gida a gareshi ganin yadda yake samun karramawa da mutuntawa a jihar ya kuma bayyana mana irin mutunci da zumunci dake tsakanin shi da shugaban hukumar Jin daɗi da walwalar Alhazzai ta jihar Kebbi.

Alh Faruku Musa Yaro Enabo Jagaban Gwandu ya kuma yi godiya da jinjina zuwa ga Maigirma Gwamnan jihar Kebbi His Excellency Comrd Dr. Nasir Idris Ƙauran Gwandu akan irin yadda yayi ɗawainiya ga Alhazzan jihar shi.

Continue Reading

Labarai

Mun gana da shugaba Tinubu mun isar masa saƙon al’umma – Shaikh Bala Lau

Published

on

Mun gana da shugaba Tinubu mun isar masa saƙon al'umma - Shaikh Bala Lau

Mun gana da shugaba Tinubu mun isar masa saƙon al’umma – Shaikh Bala Lau

Daga Idris Umar, Zariya

A ranar Alhamis tawagar malaman Najeriya ta gana da shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu dangane da halin da ƙasa ta ke ciki kan batun zanga-zanga da wasu ke ƙiran a yi dalilin halin matsi da tsadar rayuwa.

Rahoton sun nuna cewa jim kaɗanne bayan kammala ganawar, shugaban ƙungiyar Izala na ƙasa, Shaikh Abdullahi Bala Lau ya shaidawa manema labarai cewa shugaban ƙasa ya karɓi koken da suka je masa da shi.

“Mun faɗa mar halin da al’umma suke ciki na tsadar rayuwa, taɓarɓarewar tsaro da wahalar rayuwa, ya kuma ce dan Allah a ja hankalin al’umma a ba su haƙuri nan gaba kaɗan za a ga sauyi da gyara kan ƙorafe-ƙorafen da ake yi”. In ji Bala Lau.

KU KUMA KARANTA: Zanga-zanga ba gudu ba ja da baya – ‘Yan Najeriya

Daga nan kuma, Shaikh ɗin ya ja hankalin al’umma da su yi haƙuri su cigaba da addu’a, “ba mu da ƙasar da ta fi Najeriya kar mu rusa ƙasarmu da kanmu”. Inji Shaikh Bala Lau.

Continue Reading

Ilimi

Gwamnatin Katsina ta jaddada manufarta na ci gaba da bayar da horo ga malaman makaranta

Published

on

Gwamnatin Katsina ta jaddada manufarta na ci gaba da bayar da horo ga malaman makaranta

Gwamnatin Katsina ta jaddada manufarta na ci gaba da bayar da horo ga malaman makaranta

Daga Idris Umar, Zariya

Kwamishinar kula da ilimin firamare da na Sakandire ne ta bayyana ƙudirin gwamnatin jihar mai ci yanzu na ci gaba da bayar da ƙarin horo ga malamai a faɗin jihar don samar da ƙwararrun malamai da suka iya sarrafa na’ura mai ƙwaƙwalwa da za su yi gogayya da takwarorinsu a faɗin duniya.

Hajiya Zainab Musa Musawa ta bayar da tabbacin hakan ne a lokacin da ta kai ziyarar duba yadda shirin horar da malamai 10,000 da suka haɗa da sabbin ɗauka 7,000 a kan dabarun koyarwa na ƙarni na 20 ke gudana.

Kwamishinar ta kai ziyarar ne a makarantar firamare ta Modoji inda ake gudanar da bayar da horon na yini 3 wanda Ma’aikatar kula da ilimin firamare da na Sakandire, hukumar ilimin bai ɗaya da kuma haɗin gwiwa da shirin bunƙasa ilimi matakin jiha (TESS) suka shirya.

KU KUMA KARANTA: Da ilimi ake samun kowace irin nasara a rayuwa – Dauda Lawal 

Hajiya Zainab Musa Musawa wanda ta zagaya azuzuwa ta kuma tattauna da masu bayar da horon da Kuma malaman, ta bukace su da suyi amfani da lokacin su fahimci Abunda aka koyamasu don bunkasa tsarin koyo da koyarwa a jihar.

A yayin ziyarar dai Kwamishinar ta samu rakiyar Babbar Sakatariya a Ma’aikatar Hajiya Mairo Mohamed Othman, Mai baiwa Gwamna shawarma akan ilimi Nura Sale Katsayal sauran Daraktocin Ma’aikatar.

Bayanin hakan na ƙunshe a cikin wata sanarwa wadda jami’in hudda da jama’a na Ma’aikatar Malam Sani Ɗanjuma Suleiman ya Sanyama hannu a katsina.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like