Labarin yana gefen ku!

EFCC ta sake buɗe shari’ar zargin ɓatan N772bn akan Kwankwaso, Fayose da wasu tsofaffin gwamnoni 11

1

EFCC ta sake buɗe shari’ar zargin Rabi’u Kwankwaso, Ayodele Fayose da wasu tsaffin gwamnoni 11 da ke damfarar sama da N772bn.

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta kuma miƙa wa wasu tsofaffin Ministoci kuma a halin yanzu tana binciken N81.6bn da ake zargin an wawure a ma’aikatar agaji da yaƙi da fatara.

A ranar Lahadin nan ne hukumar tace wasu dala biliyan 2.2 na nufin siyan makamai domin tallafawa yaƙin da ake yi da ‘yan ta’adda amma waɗanda ake zargin sun ɓatar da su ta hanyar karkatar da kuɗaɗen tare da tsohon mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro Sambo Dasuki; marigayi ɗan jarida, Raymond Dokpesi, tsohon gwamnan jihar Sokoto, Attahiru Bafarawa; da tsohon ƙaramin ministan kudi, Bashir Yuguda da dai sauransu.

Yayin da Dasuki ke tsare a hannun jami’an tsaro na farin kaya a shekarar 2015, EFCC ta kama Dokpesi, Bafarawa, Yuguda da sauransu.

KU KUMA KARANTA: EFCC ta gurfanar da tsohon ministan lantarki, Olu Agunloye

An kama su ne bayan da kwamitin shugaban ƙasa da ya binciki sayan makamai a zamanin gwamnatin tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan ya tuhume su.

Leave A Reply

Your email address will not be published.