Connect with us

'Yansanda

DARA TA CI GIDA: Mai safarar mutane ya kashe abokiyar aikinsa, tare da sayarda sassan jikinta

Published

on

Daga Fatima GIMBA, Abuja

Wani magidanci, Dauda Bello kuma shahararren mai safarar mutane, mai shekaru 50 a duniya, ya kashe wata mata ‘yar shekara 71, Messi Adisa tare da sayar Da Sassan Jikinta ga masu harkar tsafi.

“Abokiyar aikina ce a harkar fataucin yara kafin na kashe ta.” Ya shaida wa ‘yan sanda.

Jaridar P.M.EXPRESS ta rawaito cewa jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Ogun ne suka yi nasarar kama wanda ake zargin mai suna Bello, inda aka kama shi dumu-dumu da laifin kashe marigayiya Messi Adisa, sannan ya sayar da wuya da idon sawunta ga wani matsafi, kafin bisani ya binne ta a asirce cikin wani kabari mara zurfi.

Sai dai bayan aikata wannan ɗanyan aikin, an kama shi kuma ya amsa laifin ake zarginsa da aikatawa, mummunan laifi da ke kai ga yiwa mutum hukuncin rai da rai a gidan kaso.

Jami’in hulda da jami’a na rundunar ‘yan sandan jihar Ogun, DSP Abimbola Oyeyemi ne ya tabbatar da hakan, ya bayyana cewa wanda ake zargin yana hannun ‘yan sanda ana yi masa tambayoyi tare da tsaurara bincike kan ayyukan ta’addancin da suka yi.

Da ake zantawa da shi, DSP Abimbola ya ce an kama wanda ake zargin ne a ranar Alhamis din da ta gabata.

DSP Abimbola ya bayyana cewa: “Bayan ɓacewar wadda aka kashe (dattijuwar), wadda aka gano ta bar gidanta a ranar 8 ga watan Yuni, ba ta dawo ba, hakan ya saka ‘yan uwanta korafi kan wacce ta batan.”

Bayan kama wanda ake zargin kuma ana yi masa tambayoyi, sai ya bayyana cewa ya dade da sanin wanda aka kashen, ya kuma bayyana cewa su biyun dukka ‘yan ƙungiyar harkar safarar yara ne.

Wanda ake zargin ya bayyana cewa “ya gayyaci wanda abin ya shafa zuwa gidansa ne a ranar kamar kullum, domin su tattauna harkokinsu na safara, amma da isa gidansa ya ga wani abu a tattare da ita wanda yake zargin maƙudan kudade ne.

Sakamakon haka ya bugi matar da sandar katako, domin ya karbi kudin daga hannun ta, wanda hakan ya sa ta suma, nan ya ɗauke ta zuwa daji, karshe ya kasheta ta hanyar.”

Wanda ake zargin ya bayyana cewa bayan ya caje jikin matar Naira  22,200 kawai ya gani, wanda ta karɓa ne matsayin kafin alƙalamin wani aiki. Bayan da ya gane cewa bai samu kudin da ya ke bida ba, sai ya yanke mata wuyan hannu da idon sawunta biyu, ya sayar da su ga wani matsafi domin ya sami ƙarin kudi.

Sai dai wanda ake zargin ya kai ‘yan sanda inda ya binne mamaciyar a wani kabari mara zurfi, an gano gawarta tare da kai ta wajen ajiyar gawa domin daukar rahoton gawar.

Abimbola ya bayyana cewa rundunar ‘yan sanda za ta gurfanar da duk wadanda suka aikata wannan aika-aika a gaban kuliya ta hanyar kama su tare da tuhumar su da laifin hada baki da kisan kai bayan kammala bincike.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

'Yansanda

‘Yan sanda sun kama matashin da ake zargi da yin garkuwa da ‘yar maƙocinsa

Published

on

'Yan sanda sun kama matashin da ake zargi da yin garkuwa da 'yar maƙocinsa

‘Yan sanda sun kama matashin da ake zargi da yin garkuwa da ‘yar maƙocinsa

Daga Shafaatu Dauda,Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano, ta kama wani matashi mai suna Zakariyya Muhammad, da ake zargi da laifin yin garkuwa da ƙaramar yarinya mai shekaru biyu da rabi.

Kakakin Rundunar ‘yan sandan jihar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ya aike wa da manema labarai a ranar Talata.

Sanarwar ta ce, tun a Ranar 4 ga watan Yuli 2024, rundunar ta samu ƙorafi daga wani Mazaunin unguwar Sabuwar Gandu Kwarin Barka, cewar wani ya ƙira wayar sa inda ya shaida masa cewar ya yi garkuwa da ‘yarsa mai suna Amina , har aka nemi a biya shi kuɗin fansa naira miliyan biyu kafin ya sake ta.

Bayan samun korafin ne Kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano, CP Salman Dogo Garba, ya tayar da dakarun ‘yan sanda ma su yaƙi da garkuwa da mutane, ƙarƙashin jagorancin SP Aliyu Muhammad Auwal, tare da ba Su umarnin kuɓutar da yarinyar cikin a wanni 24, da kuma kama waɗanda ake zargin.

SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ƙara da cewa, an yi nasarar kama wanda ake zargin Zakariya Muhammad , a ranar 5 ga watan Yuni 2024, inda ya tabbatar da cewar shi ne ya yi garkuwa da yarinyar sannan ya nemi kuɗin fansa.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan sanda a Kano sun ceto ’yar shekara 2 da maƙocinsu ya sace

Neptune Prime Hausa ta kawo rahotan na cewa tuni aka kuɓutar da yarinyar kuma likitoci sun tabbatar da cewar kalau ta ke.

Kakakin Rundunar ‘yan sandan Kano, ya ce an dawo da batun babban sashin binciken manyan laifuka dake Bomapai, ɓangaren da ya shafi garkuwa da mutane, kuma da zarar an kammala bincike za a gurfanar da shi a gaban kotu.

Rundunar ta ja hankalin iyaye su dinga kula da ‘ya’yansu, tare da jan kunnen matasa cewar wannan ba abin yi ba ne, kuma ba sana’a ba ce, musamman a jihar Kano domun ma su yunƙurin aikata ba su da wajen ɓuya.

Continue Reading

'Yansanda

An ja hankalin ‘yan Najeriya kan shirin ƙungiyoyin asiri na ɗaukar sabbin mambobi

Published

on

An ja hankalin 'yan Najeriya kan shirin ƙungiyoyin asiri na ɗaukar sabbin mambobi

An ja hankalin ‘yan Najeriya kan shirin ƙungiyoyin asiri na ɗaukar sabbin mambobi

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta ja hankalin ‘yan ƙasar game da shirin ƙungiyoyin asiri na ɗaukar sabbin mambobi a faɗin ƙasar musamman a jami’o’i da manyan makarantu.

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan Najeriya reshen Jihar Ribas Grace Iringe-Koko ce ta yi wannan jan hankali a cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Asabar da maraice a birnin Fatakwal.

Ta bayyana cewa wata babbar ƙungiyar asiri ta Najeriya tana shirin gudanar da gagarumin biki ranar Lahadi a faɗin Najeriya, musamman a jami’o’i don tunawa da mutumin da ya kafa ta.

“Rundunar ‘yan sandan Jihar Ribas ta samu bayanai game da bikin da ƙungiyar Neo-Black Movement (NBM) za ta yi a faɗin ƙasar ranar 7 ga watan Yulin 2024. Ƙungiyar, wadda ake yi wa laƙabi da Aiye ko Black Axe, tana shirin gudanar da bikin ne domin tunawa da wanda ya kafa ta.

KU KUMA KARANTA: Shugaban hukumar leƙen asirin sojin Isra’ila ya yi murabus saboda harin Hamas na 7 ga Oktoba      

Bikin, wanda aka sanya wa suna Ranar AIYE ko 7/7 za a gudanar da shi ne a dukkan jihohin da ke faɗin ƙasa, musamman a manyan makarantu,” in ji sanarwar.

An gargaɗi masu ta da hankalin jama’a a Bikin Dodanni na Egungun a Jihar Oyo

Rundunar ‘yan sandan ta ce tana sane da munanan ayyukan ƙungiyar asirin na kisan mutane a manyan makarantu da faɗace-faɗace a tsakanin ƙungiyoyin asiri da tayar da zaune-tsaye da sauran manyan laifuka.

Ta ce yanzu haka ta baza ƙarin jami’an ‘yan sanda zuwa wasu wurare domin daƙile ayyukan ƙungiyoyin asiri, sannan ta yi ƙira ga iyaye su gargaɗi ‘ya’yansu su guji shiga ayyukan ƙungiyoyin asiri.

“Ana bai wa manyan makarantu shawarar ƙara matakan tsaro da kuma sanya idanu sosai domin tabbatar da tsaron dukkan ɗalibai.

Kazalika ana ƙira ga dukkan makarantu su lura da duk wani taro na ɗalibai da bai kwanta musu a rai ba,” a cewar sanarwar.

Continue Reading

'Yansanda

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Published

on

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tube wa wasu jami’an ta biyar kaki sakamakon zargin su da karɓar cin hancin kuɗi kimanin Naira miliyan uku.

Mataimakin Shugaban ’yan Sanda mai kula da Shiyya ta shida ta da ke Jihar Kuros Riba, Jonathan Towuru, ya sanar a Kalaba cewa ’yan sandan sun kwace kuɗin ne da bakin bindiga a hannun wani mai abin hawa.

A makon jiya ne aka zargi jami’an da ƙwayar kuɗin da bakin bindiga a hannun wani mutum da rundunar ta sakaya sunansa.

Yanzu haka waɗanda ake zargin an tuɓe masu kaki amma ana tsare da su ana bincike, da zarar an same su da laifi kotu za a turasu ta yanke masu hukuncin da ya dace.

KU KUMA KARANTA: ’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Mataimakin shugaban ’yan sandan ya ce waɗanda ake zargin su da karɓar cin hancin kuɗi Naira milyan uku daga wannun wani.

Ko a kwanan baya irin haka ta taba faruwa a kan babbar hanyar Kalaba zuwa Ikom inda aka kama wasu ’yan sanda kan karbar na goro.

Tafiya a kan hanyar na yawan zargin ’yan sanda da kula da shingen bincike a kan hanyar da yawan tatsar su kuɗi.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like