Connect with us

Labari

Dan Takarar Gwamnan APC Ya Shiryawa ‘Yan Jaridu Bude Baki A NUJ Kaduna

Published

on

Daga; USMAN NASIDI, Kaduna.

DAYA daga cikin yan takarar Kujerar Gwamnan Jihar Kaduna a karkashin Jam’iyyar APC, Dakta muhammad Abdulmalik Durunguwa ya shirya yan Jaridu bude baki na musamman domin nuna kulawarsa agaresu bisa kokarinsu, jajircewarsu, da sadaukarwar domin tabbata al’amura sun cikin nasara a Jihar da kasar baki daya.

Dan takarar wanda ya Jagoranci wata tawagar izuwa wajen taron bude bakin wanda ya gudana a sakatariyar Kungiyar NUJ dake Kaduna, ya samu halartar yan Jaridu da dama Musulmai da Kiristoci maza da mata inda aka ci aka sha, kana aka gabatar da jawabai na karin dankon zumunci da fahimtar Juna a tsakaninsu.

Da yake jawabi bayan kammala shan ruwan a wajen taron, dan takarar Kujerar Gwamnan ya bayyana cewa ya shirya wannan zaman na musamman ne domin karrama yan Jaridun bisa kokarin da suke da irin jajircewarsu akoyaushe, sannan da nuna kaunar shi a gare su a matsayin tsohon abokin huldarsu a sakatariyar Kungiyar ta Jihar.

Durunguwa, ya kara da cewa shi mutum ne wanda ya dade yana hulda da mutane da yanayin hulda da mutane wanda hakan ya bashi damar kai wannan ziyarar tare yin bude bakin a cibiyar Kungiyar domin neman goyon bayansu a bisa kudirinsa na tsayawa Takarar shugabancin Jihar a matsayin Gwamna.

Ya ce “ni dan Kaduna ne kuma haifaffen Kaduna kuma dan Kudancin Kaduna wanda yasan lungu da sako na Jihar don haka ba wani abun da wani zai fada mun dangane da ciki da wajen Jihar Kaduna don haka ina kalubalantar duk wani da zai yi yunkurin ganin bata mana kasa.”

“Na fi kowa sanin abinda da mutanen karkara ke so ko suka fi bukata don na sha mangoro a titi, nayi wanka a rafi, naje farauta a daji don haka mene ne ake so, hakazalika nasan abubuwan da mutanen birni ke so, don haka nasan meye fanka kuma nasan meye iska mai dadi a daji, toh ashe kuwa ba wani zai fada mun komai.

“Burina kawai shi ne na tabbatar da mutumin Jihar Kaduna ko a Birni ko a daji a matsayin mutumin karkara, kana iya kwana lafiya ka tashi lafiya, kaje gonarka, ka cire amfanin gonar, kaje Kasuwa ka sayar ka sayo abin da kake so, kana ka dawo gida ka zaune lafiya cikin kwanciyar hankali kaci abun ka yadda kake so ba tare da tashin hankalin ba, wannan shi ne Babban burina.”

Acewarsa, idan al’ummar Jihar zasu ba shi dama, zai yi amfani da sashen Noma wajen yin amfani ya Farfado da tattalin arzikin Kasar baki daya bama Jihar kadai ba kana daga arzikin da suke da shi a Jihar tun da Allah Ya albarkace su da arziki musamman a Kudancin Kaduna.

Da take jawabin maraba bisa ga Dan takarar bisa shirya wannan bude bakin da ya yi tare da su, Shugaban Kungiyar Yan Jaridu (NUJ) reshen Jihar Kaduna, Kwamared Asma’u Yawo Halilu, ta yaba wa Dan takarar bisa wannan dama da ya basu, kana ta gode mishi bisa kokarin ya nuna karamci gare su.

Hajiya Asma’u, ta kara da cewa kungiyar za ta cigaba da tsayawa kai da fada wajen ganin ta aiwatar da duk wani aikin daya dace ta fuskar kwarewa a tare da duk ma’aikatansu, wanda a halin yanzu tuni sun yi nisa wajen ganin sun hada kan duka yan Jaridun tare kawata aikin.

A Karshe, Shugabar kungiyar ta NUJ, ta jinjinawa Dan Takarar bisa nuna kaunar da ya yi musu kasancewar shi ne mutum na farko da ya fara zuwa ziyartarsu da kam shi, kana har da shirya musu wata kwarya-kwaryar zaman shan ruwan na bude bakin Azumi watan Ramadana.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like