Connect with us

Labari

Dalilan EFCC Na Gurfanar Da Rochars Okorocha Gaban Kuliya

Published

on

Ana dai zargin Rochas da hada baki da wasu kamfanoni guda biyar da wani dan siyasa daga jam’iyyar APC mai suna Anyim Nyerere Chinenye da wawure kudaden gwamnati a cikin tuhume-tuhume 17 da hukumar ta EFCC ta shigar babbar kotun tarayya da ke Abuja a jiya LitininABUJA, NIGERIA — 

Hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa EFCC a Najeriya ta gurfanar da tsohon gwamnan jihar Imo kuma Sanata mai ci a yanzu Rochas Okorocha bisa zargin sama da fadi da kudaden gwamnati da suka kai Naira biliyan 2.9

Hakan na zuwa ne sa’o’i kadan bayan da tsohon gwamnan ya fito a hukumance ya ayyana niyarsa ta tsayawa takarar shugaban kasa a shekarar 2023.

Ana dai zargin Rochas da hada baki da wasu kamfanoni guda biyar da suka hada Naphtali International Limited, Perfect Finish Multi Projects Limited, Consolid Projects Consulting Limited, Pramif International Limited, da Legend World Concepts Limited tare da wani dan siyasa daga jam’iyyar APC mai suna Anyim Nyerere Chinenye wajen wawure kudaden cikin tuhume-tuhume 17 da hukumar ta EFCC ta shigar babbar kotun tarayya da ke Abuja a ranar Litinin.

A zantawar da Muryar Amurka ta yi da shugaban hukumar EFCC Malam Abdulrashid Bawa, ya bayyana cewa tun ba yanzu ba hukumar ke bincike akan Rochas wanda aka ba da belinsa bayan tsare shi da ta yi.

Ya kara da cewa ko a watan Afrilu na shekarar 2019 sai da aka tsare shi na tsawon kwanaki biyu don amsa tambayoyi bisa zargin almundahana da kudaden gwamnati.

Kazalika a watan Agustan 2019, sai da hukumar EFCC ta sake tsare Sanatan don amsa wasu karin tambayoyi bayan ta gano wasu kadarori da suka hada da gidajen zama, makarantu, da kasuwanni da dai sauransu dake da alaka da shi.

Daga cikin kadarorin da hukumar ta rufe a lokacin sun hada da makarantar Rochas Foundation College dake Owerri, East High Primary and Secondary School a Owerri wacce ‘yarsa ta farko mai suna Uloma Nwosu ke lura su da kuma babban katin siyayya ta All-In Supermarket a garin Owerri duk a jihar ta Imo.

Idan za’a iya tunawa gabanin lokacin zaben shekarar 2019 da ya gabata sai da hukumar EFCC ta tuhumi Okorocha bisa zargin fitar da sama da Naira biliyan 1 daga asusun gwamnatin jihar don taimakawa yakin neman zaben surukinsa Uche Nwosu, a lokacin zaben gwamnan jihar ta Imo.

lamarin da ya kai da Hukumar ta kuma kama Akanta-Janar na jihar, Uzoho Casmir, bisa zargin taimakawa Okorocha wajen cire kudaden

Sai dai a bangaren Rochas kuwa ya karyata zarge zargen da hukumar ta yi mishi a wata hira da gidan talabijin na Channels ya yi da shi yana mai cewa Maimakon a tuhume shi da laifin cin hanci da rashawa, shi ya kamata ya gabatar da kararsa na kin biyansa hakkokinsa a lokacin yana gwamna na tsawon shekaru takwas.

Ko da yake Okorocha ya bayyana cewa wannan ba shi ne karon farko da ya ke fuskantar irin wannan cin zarafi daga hukumar EFCC ba, yana mai cewa siyasa ce kawai da bita da kulli

Sai dai kuma tsohon gwamnan ya shawarci hukumar EFCC da kada ta bari ta zama makamin ‘yan siyasa amma ta binciki zarge-zargen sannan ta samu hakikanin gaskiya kafin daukar matakan da suka dace.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like