Connect with us

Labari

Burina Gina Samuwar Jihar Zamfara Da Kowa Zai Yi Alfahari Da Ita- Gwamna Matawalle

Published

on

Daga IMRANA ABDULLAHI Kaduna

Gwamnan Jihar Zamfara Dokta Bello Muhammad Matawalle ya bayyana cewa babban kalubalen da ke gaban duk wani ma’aikacin Gwamnatin Jihar Shi ne yin aiki tukuru bisa tsarin bin doka da ka’ida domin ciyar da Jihar gaba.

Gwamna Muhammad Bello Matawalle ya tabbatar da cewa kalubalen da ke gabansa shi ne ya samu cika burinsa na samar da Samuwar Jihar Zamfara da kowa zai yi alfahari da ita.

Gwamnan ya yi kira ga daukacin ma’aikatan Jihar da su kara rubanya kwazon aiki wajen ganin an gina sabuwar Jihar Zamfara mai inganci da yaya, Jikoki za su yi tunkaho da ita.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a wajen taron bude samar da horaswa na kwanaki biyar ga jami’an Gwamnatin Jihar da aka yi a garin Abuja.

Taron mai taken samar da kyakkyawan shugabanci domin ci gaba an shirya shi ne tsakanin Gwamnatin Jihar tare da hadin Gwiwar wata makarantar Koyar da dabarun kasuwanci da le Ibadan.

Gwamna Matawalle ya ci gaba da bayanin cewa “ina kara jadda kira a gare ku da ku kara zage damtse wajen dadewa domin mu kawar da matsalar yan bindiga da nufin samar da Jiha ingantacciya da ke kan hanya dai dai da kowace Jiha ta hanyar aikinta arzikin da Allah ya ba mu a cikin Jihar.

Gwamnan ya lissafa wa mahalarta taron wadansu muhimman al’amuran da Gwamnatinsa Gwamnatinsa Sanya a gaba da nufin tsare gaskiya da adalci wajen tafiyar da aikin Gwamnati.

“Ina murna da farin cikin shaidawa duniya cewa dokar hana bautar da kananan yara da kuma ta kara inganta rayuwar masu bukata ta musamman da zarar an kawo ta gabana San Sanya wa dokar hannu”, Inji Gwamna Matawalle.

Kafin in kammala jawabi na ina son yin amfani da wannan dama in bayyana farin ciki da murna ga shugabar ma’aikatan Gwamnatin tarayya uwargida Folashade Mejabi Yemi – Esan, bisa kokarin da ta yi na halartar wannan taro duk da irin dimbin ayyukan da ke gabanta amma ta halarci wannan taron da kanta.

“Hakika wannan babban taro ya zo a lokacin da ya dace saboda Jihar Zamfara na matukar bukatar kwararru kuma hazikan mutanen da za su gudanar da aikin ci gaban Jihar.

An dai shirya taron ne ga kwamishinoni,Masu bayar da shawara,da kuma jami’an Gwamnatin Jihar Zamfara a ranar 17 ga watan Janairu 2022 a otal din rock view da ke Abuja.

Ni ɗan jarida ne mai zaman kansa. Mawallafi kuma mai sharhi a lamarin yau da kullum.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like