Connect with us

Labarai

Bayan Shekaru tara, Sojoji sun sake kuɓutar da ‘yar makarantar Chiɓok guda ɗaya

Published

on

Dakarun Bataliya Taskforce 114 dake Bita a jihar Borno sun sake kuɓutar da wata ‘yar makarantar Sakandiren Chiɓok guda ɗaya wadda aka sace tare da wasu sauran ɗalibai a ranar 14 ga Afrilu, 2014.

A ranar 21 ga watan Afrilun 2023 ne sojojin suka ceto Hauwa Maltha mai shekaru 26 mai lamba ta biyu a jerin ‘yan matan makarantar Chiɓok da aka sace tare da jaririnta mai shekaru uku a lokacin da suke gudanar da wani samame a Lagara.

Ta fito daga ƙabilar Kibaku dake Jila a ƙaramar hukumar Chiɓok ta jihar Borno. Yayin da take tsare, Hauwa ta yi aure a Gulukos da wani Salman, mai ɗaukar hoto ga marigayi shugaban ta’addanci, Shekau.

Daga baya Salman ya rasu a tafkin Chadi. Daga nan sai Hauwa Maltha ta sake yin aure da wani Malam Muhammad a garin Gobara ta haifa masa ‘ya’ya biyu.

KU KUMA KARANTA: An sake ceto ƴan matan Chibok biyu a Jihar Borno

An kuma kashe Malam Muhammad, mijin ta na biyu a Ukuba da ke dajin Sambisa a lokacin da aka yi artabu tsakanin ‘yan ƙungiyar JAS/ISWAP.

Tun bayan ceto Hauwa, wadda ita ma tana ɗauke da cikin kimanin wata takwas da sati biyu, an yi mata cikakken binciken lafiya tare da jaririnta.

Bayan an farfaɗo da su yadda ya kamata, Hauwa da jaririyarta, Fatima, za a miƙa su ga gwamnatin jihar Borno domin ci gaba da gudanar da rayuwa.

3 Comments

3 Comments

  1. Pingback: Sojojin Najeriya sun musanta zargin yin sulhu da matasan kiristocin kudancin Kaduna | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: Sojojin Najeriya suna da karfin daƙile tayar da ƙayar baya – COAS | Neptune Prime Hausa

  3. Pingback: An sace ɗalibai ‘yan makaranta 1,683 cikin shekaru 8 a Najeriya – Rahoto | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like