Connect with us

Labari

Ba Zamu Amince Da Cin Mutuncin Yan Arewa A Jihar Ondo Ba – Shattima Yerima

Published

on

Daga; MUSTAPHA IMRANA ABDULLAHI.

KUNGIYAR matasa masu tuntuba ta arewacin Najeriya (AYCF) ta gargadi Gwamnan Jihar Ondo, Rotimi Akeredelu “bisa iron yadda a kwanan nan aka rika gallazawa yan Arewa a Jihar”.

Bayanin hakan na kunshe ne a cikin wata takardar da ke dauke da sa hannun shugaban kungiyar na kasa kwamared Shattima Yerima, inda ya ankarar da Gwamnan a cikin takardar cewa ya dace fa Gwamnan ya duba sosai da idanun basira irin yadda lamura ke faruwa ga yan Arewa a Jihar ta Ondo.musamman yadda yayan kungiyar Amotekun ke kama wa tare da tsare yan Arewa da ke gudanar da harkokinsu a cikin Jihar.

Kungiyar tuntuba ta AYCF a cikin takardar da ta raba wa manema labarai ta kalubalanci irin yadda lamarin ke faruwa, abin da kungiyar ta bayyana da cewa “wadansu mutane dauke da makamai da suke labewa tamkar su jami’an tsaro ne kuma a cikin kasar da akwai jami’an Yan Sanda, da Yan sandan farin kaya na DSS da kuma jami’an tsaron farin kaya na NSCDC, da sauransu wadanda su ne kawai ke kunshe a cikin dokar kasa da aka amincewa su yi aiki bisa dokar kasa”.

Kungiyar sai ta ci gaba da cewa ” muna aikawa da gargadi da kakkausar murya ga Gwamnatin Jihar Ondo da su daina rufe idanuwan ta a game da irin yadda ake kaiwa yan Arewa hari duk da cewa yan Najeriya ne masu cikakken yanci da suke gudanar da harkokinsu na saye da Sayarwa da ayyukan da dokar kasa ta amince da su ayi a cikin jihar”.

Ya dace Gwamna, Gwamnati da jama’ar Jihar Ondo su Sani cewa “idan sauran al’ummar yankin arewacin Najeriya sun dauki irin wannan matakin na cin mutunci, matsin lamba ga yan asalin Jihar Ondo, da a yanzu ba za a samu wani dan asalin Jihar Ondo ya na zaune a arewacin Najeriya ba, ko ya na zaune ko kuma ya rika gudanar da harkokin kasuwanci”, inji Shattima Yerima shugaban Gwagwarmaya.

” saboda haka ya dace Gwamnan ya dauki matakan da ya dace”.

Kungiyar AYCF sai ta fayyace karara a fili cewa; “mun gashi da irin wannan wulakanci da cin mutuncin da ake yi wa jama’ar Arewa a Jihar Ondo don haka kamar yadda muka bayyana yin da farko muna bukatar Gwamna ya dauki matakan kawo karshen wannan lamarin kowa ya samu kwanciyar hankali da walwala cikin lumana”.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like