Connect with us

Kungiyoyi

AYCF Ta Ankarar Da Majalisar Dokoki, DSS Bisa Zargin Son Zuciya Na Karin Girman Hukumar Kwastan

Published

on

Daga; MUSTAPHA IMRANA ABDULLAHI.

SAKAMAKON irin rade- radin da ake yi kuma suna kara bazuwa cewa rundunar hukumar kwastan ta Najeriya na kokarin cire wadansu Jami’anta da aka dauka aiki kafin shekarar 2009 daga jadawalin wadanda za a yi wa karin girma.

Hakan ya sa kungiyar matasa masu tuntuba ta Arewa (AYCF) ke yin kira ga Jami’an Tsaron Yan Sandan farin kaya na DSS da su hanzarta kama aiki a game da wannan batun domin hukumar gudanarwar Jami’an kwastan masu yaki da yan fasa kauri su yi abin da ya dace.

Wannan na kunshe ne a cikin wata takardar da ke dauke da sa hannun shugaban kungiyar AYCF na kasa Alhaji Shettima Yerima, wanda aka rabawa manema labarai a ranar 27 ga watan Fabrairu, 2022.

Ya ce “Muna yin kira ga daukacin majalisar dokoki ta kasa da su hanzarta shiga wannan maganar domin a kwatowa mama’s Hakkinsu, domin ganin wannan lamarin mai sarkakiya da kuma mummunan hadari na yin zabi sonka bai kai lamari ba.

Saboda kasancewar hukumar kwastan mai matukar muhimmanci ga harkokin tsaron kasa, muna ganin cewa hukumar tsaron Yan Sandan farin kaya ta DSS ya dace su kasance a cikin gudanar da wannan al’amarin aikin karin girma ga ma’aikatan kwastan wanda yakasance za a yi masa sakayya ne ga irin abin da suka aikata na yin aiki tukuru”, inji shi.

Kungiyar ta AYCF ta ci gaba da bayanin cewa wannan matakin da suka dauka sun yi ne da nufin ganin an yi wa kowane ma’aikaci adalci a wajen batun karin girma a duk lokacin da hakan ya taso,

“Mun samu tattara bayanai cewa an shirya za a cire wadansu mutane ne a wajen batun yin karin girman musamman wadanda aka dauka aikin kwastan daga shekarar 2009 da 2015.

“Hakika yin irin hakan ba dai dai ba ne domin akwai ma’aikatan wannan hukumar da suka dade suna yin aiki na tsawon shekaru da yawa har masu shekaru 30 akwai”.

“Wannan matakin da hukumar kwastan ke dauka na nuni ne da cewa mahawarar da ake ta tafkawa a game da yadda ba a samu damar daukar wasu sababbin ma’aikata ba daga shekarar 1992 da 1994, har sai a 2009 lokacin da Gwamnatin Goodluck Jonathan da janye dokar hana daukar sababbin ma’aikata”, kamar yadda suka ce.

Kungiyar AYCF ta ce bisa dogaro da irin sahihan bayanan da ta samu, sun cimma matsaya kamar haka da suke fatan za a duba sosai da idanun basira;

  1. Cewa irin gibin da aka samu sakamakon tazara mai tsawo dalilin Sanya dokar yin hani a dauki ma’aikata, ba laifin ma’aikatan hukumar kwastan ba ne da suka bayar da duk wata damar da suke da ita tun daga karfi, tunaninsu da jinin jikinsu a wajen gudanar da aikin domin kasa ta ci gaba har na tsawon shekaru sama da Talatin (30).
  2. Saboda haka bamu amince da hakan ba domin babu wanda zai yarda da hakan sam sam, duk wani tsarin da za a yi amfani da shi wajen yi wa jami’an hukumar kwastan katin girma ba dai ta bayan gida ba dole ne abi doka da ka’ida kawai.

3.Mun yi tsammanin cewa tsarin ganin mutunci da girmam juna da ya kasance shi ne tsarin shugaba Muhammadu Buhari, wannan ne aka Sani da shi, ya dace ayi amfani da hakan domin tabbatar da an yi wa kowa adalci

4.Hakika hankalin mu ya tashi duk min damu ganin irin yadda wannan hukumar ta kasa bin doka da ka’idar yi wa jama’a karin girm duk da cewa akwai tsarin da tanajin dokar kasa ta tanadar a kan yin hakan amma an yi biris da shi.

  1. Kuma lamari ne abin ban kinya kwarai hukumar kwastan ta rika aiwatar da irin wannan da ya sabawa dokar kasa, ba kuma tare da yin aiki da ofishin ministan kudi da tsare tsare ba, ko kuma neman shawara daga ofishin shugaban ma’aikata na kasa ba ko kuma Sakataren Gwamnatin tarayya ba”.
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Kungiyoyi

Ƙungiyoyin musulunci sun raba wa marayu 900 abinci kyauta a Katsina (Hotuna)

Published

on

Daga Abbas Bamalli

A wani biki mai ƙayatarwa da aka gudanar a gidan marayu na Katsina, sama da marayu 900 ne suka sami farin ciki matuƙa a lokacin da suka samu liyafar cin abincin rana, wanda ƙungiyoyi masu zaman kansu na Musulunci na ƙasa da ƙasa suka yi shirya.

Amir Sultana daga ƙasar Turkiyya tare da haɗin gwiwar Munazzama Da’awa Al-Islam (MADA) daga ƙasar Sudan ne suka shirya taron tare da haɗin gwiwar ofishin uwargidan gwamnan jihar Katsina, Hajiya Zulaihat Raɗɗa.

Shugaban ƙungiyoyi masu zaman kansu, Mufti Ahmed, ya bayyana cewa kimanin marayu 700 a ƙaramar hukumar Katsina da 200 a Jibiya ne suka ci gajiyar wannan kyakkyawan shiri.

Ahmed ya jaddada cewa manufarsu ita ce sanya murmushi a fuskokin marasa galihu, musamman marayu, da ke nuna irin yadda ƙungiyoyin ke gudanar da ayyukan jin ƙai.

KU KUMA KARANTA: Zulum ya raba wa iyalai dubu 40 tallafin abinci da kuɗi a Konduga

An samo kuɗaɗe don shirin ne ta hanyar gudumawa daga mawadata da ɗaiɗaikun mutane da suka amince da ƙungiyoyi masu zaman kansu.

Mufti Ahmed ya bayyana cewa, “Ta hanyar tallafin mun gina rijiyoyin burtsatse kusan 36 a wurare daban-daban a jihar.”

Ya ci gaba da cewa, “Yana daga cikin shirinmu na yin amfani da ragowar kuɗaɗen wajen sanya murmushi a fuskokin marasa galihu, musamman marayu a cikin al’ummarmu.

Wani ɓangare na ayyukanmu shi ne rarraba Alƙur’ani mai girma da kuma bayar da tallafin kuɗi ga marasa galihu.” Baya ga cin abincin rana, ƙungiyoyin sun kuma bayar da gudummawar dalar Amurka 400 ga marayun, wanda hakan ya ƙara haɓaka tasirin ayyukansu na alheri.

Alhaji Isah Muhammad-Musa, kwamishinan ayyuka na musamman, ya yaba da wannan mataki na ƙungiyoyi masu zaman kansu, inda ya ce hakan ya ƙarawa ƙoƙarin Gwamna Dikko wajen tallafawa marasa galihu da marayu a jihar.

Ya bayyana cewa, uwargidan gwamnan ta shirya yin irin wannan aikin na jin ƙai nan ba da jimawa ba, tare da ƙara azama wajen ɗaukaka masu buƙata a cikin al’umma.

Kalli hotona a nan:

Continue Reading

Kungiyoyi

Za a yi taron ƙasashen Musulmai da na Larabawa a Saudiyya kan yaƙin Gaza

Published

on

Saudiyya ta ce za ta karɓi baƙunci taron ƙungiyar Haɗin Kan Ƙasashen Musulmai don tattauna yaƙin Gaza

Ministan zuba jari na ƙasar Saudiyya ya ce, nan da kwanaki masu zuwa ƙasar za ta karɓi baƙuncin taron koli na ƙasashen Larabawa da ƙasashen Musulmai domin tattaunawa kan yaƙin Isra’ila da Falasɗinu.

“Za mu gani a cikin ‘yan kwanaki masu zuwa, Saudiyya ta ƙira wani taron gaggawa na Larabawa a Riyadh,” in ji ministan zuba jari na Saudiyya Khalid Al-Falih, a taron Bloomberg New Economy Forum a Singapore.

KU KUMA KARANTA: An harba rokoki daga Gaza zuwa Tel Aviv

“A cikin kankanin lokaci, makasudin gabatar da waɗannan tarukan guda uku da sauran tarukan ƙarƙashin jagorancin Saudiyya shi ne a kai ga warware rikicin cikin lumana.”

Kamfanin dillancin labaran Etemad ya rawaito cewa, shugaban ƙasar Iran Ibrahim Raisi zai tafi Saudiyya a ranar Lahadi mai zuwa don halartar taron kolin Ƙungiyar Haɗin kan Ƙasashen Musulmai, wadda ita ce ziyarar farko da wani shugaban ƙasar Iran ya kai tun bayan Tehran da Riyadh suka kawo ƙarshen rashin jituwar da aka shafe tsawon shekaru ana yi ƙarƙashin wata yarjejeniya da China ta kulla a watan Maris.

Continue Reading

Jan hankali

Sun yi wa likita dukan kawo wuƙa saboda ‘yar uwarsu ta rasu a Asibiti

Published

on

A ranar Talata ne wani mutum da ɗansa suka fusata inda suka sauke fishin su akan wani babban likita da ma’aikaciyar jinya a cibiyar kiwon lafiya ta tarayya da ke Idi-Aba, Abeokuta bayan da ‘yar uwansu ya rasu a cibiyar.

Rikicin ya ɓarke ne da misalin ƙarfe 2:00 na safiyar ranar Talata, a sashen bayar da agajin gaggawa na asibitin jim kaɗan bayan wata mara lafiya mai shekaru 53 ta rasu.

Shugaban ƙungiyar likitocin Najeriya reshen jihar Ogun, Dakta Kunle Ashimi yayin da yake zantawa da manema labarai, ya yi Allah wadai da harin da ‘yan uwan mamaciyar suka kai wa biyu daga cikin ma’aikatan jinya,akan mutuwar matar a sakamakon ciwon zuciya.

KU KUMA KARANTA:Lauya ya yi wa tsohon mijin wacce yake karewa duka a kotu

Ashimi ya ce Dr Pelumi Somorin likitan ne wanda abin ya shafa,yayin da ba a tantance ko waye ma’aikaciyar jinya ba.

Ya bayyana cewa mahaifin da ɗan, sun mari likitan yayin da aka sanar da su mutuwar yar uwar su.

A cewar Ashimi, matar ‘yar shekara 53 da aka kawo asibitin da ciwon zuciya mai tsanani, wanda ita kanta bayan binciken da ta kawo daga cibiyar da aka turo ta, ya nuna cewa,ba za ta ɗauki fiye da kwana ɗaya ba, sai dai wani ikon Allah.

“Watau ta kasance a matakin ƙarshe na gazawar zuciyarta. An bayyana hakan ga ’yan uwan ta, lokacin da aka kawo ta wurin, amma duk da haka mun yi imanin cewa,Allah kan iya yin wani abu, kuma muna jin cewa ya kamata mu yi iya ƙoƙarinmu don ganin mun taimaka mata.

“Ya taɓa faruwa a baya cewa, wani mutum da ke cikin irin wannan yanayin ya samu sauki tare da kulawar da ta dace.

“Amma abin takaici, wannan majinyaciyar ta mutu da misalin karfe 2 na safe kuma mijin da ɗan marigayiyar suka faɗa kan likitan da ke kula da mara lafiyar lokacin da aka sanar da labarin rasuwarta.

“Sun mari likitan , daga baya kuma suka hau matar mutanen da ke kusa da su suka yi ta jibgarta.

“Waɗannan mutanen kuma sun ci mutuncin wata ma’aikaciyar jinya” in ji shi.

Shugaban ƙungiyar ya ce an sanar da ‘yan sanda game da lamarin, inda ya ƙara da cewa duk da kasancewar ‘yan sanda a wajen,ɗan ya ci gaba da cin mutuncin su.

“An kira ‘yan sanda kuma DPO na ofishin ‘yan sanda na Kempta ya jagoranci tawagar ‘yan sanda zuwa wurin.

“Duk da kasancewar ‘yan sanda, ɗan mamacin ,ya afkawa wata ma’aikaciyar jinya kuma duk ƙoƙarin kwantar da hankalinsa da aka yi, ya ci tura.

“A karshe an kai mutanen biyu zuwa ofishin ‘yan sanda na Kemta, inda aka ɗauki bayanansu da na likitan da aka kai wa harin, ma’aikacin jinya da kuma shaidun da ke kewaye.”

Shugaban na NMA, ya gargadi ‘yan Najeriya da su daina cin zarafin ma’aikatan kiwon lafiya, yana mai shan alwashin cewa, duk wanda aka samu da laifi za a gurfanar da shi a gaban kotu.

“Mun yanke shawarar cewa wannan zai zama na ƙarshe kuma ba za mu yadda a bamu haƙuri ba, mun yanke shawarar mika ƙarar zuwa kotu kuma gobe za mu kasance a kotu.

“An fara duk wata shari’a kuma za mu kai wannan ƙara kotu.

“Muna so mu yi kira da kuma gargaɗi ga duk waɗanda suke zuwa asibitoci a Ogun cewa ƙungiyar likitocin Najeriya, da sauran abokanta da kowane likita, ba za su amince da kalmar “ayi hakuri” nan ba daga yanzu, daga duk wanda ya zagi wani daga cikin membobinmu.

“Za mu yi iya bakin kokarinmu wajen gurfanar da irin waɗannan mutanen kuma ba za mu amince da rokon kowa ba komai girman mutum.

“Don haka, muna rokon duk wanda yake da hankali ya yi tunanin zai iya roƙon mu daga baya don faranta ran jama’a. Ba laifinmu bane”.

Ashimi ya jaddada cewa, cin zarafin ma’aikatan lafiya ya zama ruwan dare gama duniya, wanda har yanzu ba a warware shi ba duk da kamfen da aka yi na daƙile barazanar.

Ya ce “a duniya baki daya, wannan batu ne da ke ci gaba da gudana kuma an gudanar da yakin akan hana hakan, da dama a duk faɗin duniya na yakar tashe-tashen hankula da cin zarafi da ake yi wa ma’aikatan lafiya.

“Musamman a cibiyar kiwon lafiya ta tarayya a Abeokuta, jihar Ogun da sauran asibitocin da ke kewayen Jihar Ogun waɗanda ke ƙarkashin ikonmu a matsayin kungiyar likitocin Najeriya.

“Mun gudanar da yaƙi da hani,da irin halayyar nan, da dama a kan wannan taron a baya kuma bayan yawan rokon da muka yi, sai da muka roƙi likitocinmu da su karɓi uzurin waɗanda suke yin abun

“Abubuwa irin wannan ba sa raguwa, a zahiri, wannan yana faruwa sau da yawa a lokuta da dama.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like