Connect with us

Labarai

An kama mutum 8 kan zargin kashe malami a Jami’ar Maiduguri

Published

on

Rundunar ƴan sandan jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya ta ce ta kama mutum takwas da ake zargi da hannu a kisan wani malamin Jami’ar Maiduguri a ƙarshen makon jiya.

Mai magana da yawun rundunar, Daso Kenneth, ya shaida wa manema labarai cewa an kama mutanen ne bayan sun samu bayani daga shugaban jami’in tsaron Jami’ar.

Bayanai sun ce an kashe Dokta Kamal Abdulkadir, malami da ke koyarwa a Sashen Ilimin Motsa Jiki da Kula da Lafiya (Physical and Health Education), a ofishinsa.

Kakakin ƴan sandan ya ce shugaban jami’in tsaron jami’ar ya gabatar musu da ƙorafi cewa an ga wata gawa wadda daga bisani aka tabbatar ta Dokta Abdulkadir Kamal ce.

KU KUMA KARANTA: Sojojin Najeriya sun kashe ƴan ta’adda da yawa a Katsina da Zamfara

Ya ce nan-take suka aika jami’ansu wurin da lamarin ya faru inda suka ɗauki gawar zuwa asibiti domin yin bincike.

Daso Kenneth ya ce mutanen da suka kama sun soma taimaka musu wurin bincike a yayin da suke farautar ƙarin mutane da ake zargi da hannu a kisan malamin jami’ar.

Kawo yanzu ba a san musabbabin kisan malamin ba, sai dai wasu rahotanni sun ce an ga alamun raunuka sakamakon wuƙar da aka caccaka masa sannan aka sace motarsa.

Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

‘Yan sanda sun sha alwashin daƙile tashe-tashen hankula a lokacin zanga-zanga

Published

on

‘Yan sanda sun sha alwashin daƙile tashe-tashen hankula a lokacin zanga-zanga

‘Yan sanda sun sha alwashin daƙile tashe-tashen hankula a lokacin zanga-zanga

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta sha alwashin magance tashe-tashen hankula yayin zanga-zangar gama garin da ake shirin gudanarwa a ranar 1 ga watan Agusta mai kamawa.

Sanarwar da kakakin rundunar ‘yan sandan birnin tarayya Abuja, SP Josephine Adeh, ta fitar a yau Juma’a tace, rundunar ta tura jami’anta dubu 4 da 200 domin shawo kan duk wani nau’in tashin hankalin da ka iya tasowa yayin zanga-zangar.

Manufar tura ‘yan sandan ita ce tabbatar da tsaron al’umma da ba da kariya ga masu zanga-zangar.

KU KUMA KARANTA:Ba za mu bari a wargaza ƙasa ta hanyar zanga-zanga ba – Rundunar Sojin Najeriya

Da ya ke tabbatar da hakkin mazauna birnin na gudanar da zanga-zanga, kwamishinan ‘yan sanda Abuja, Benneth Igweh, ya ba da shawarar cewa kamata ya yi a yi ta cikin lumana.

Ya ce, “kwamishinan ‘yan sanda ya sha alwashin daƙile dukkanin wani nau’i na tashin hankali da rashin bin doka da oda, kasancewar ‘yan sanda ba zasu kyalle suna kallo a lalata dukiyoyin hukuma da na daidaikun mutane ko kuma a samu asarar rayuka ba.

Continue Reading

Labarai

Sarkin Gwandu ya naɗa ɗan Buran ɗin Gwandu babba

Published

on

Sarkin Gwandu ya naɗa ɗan Buran ɗin Gwandu babba

Sarkin Gwandu ya naɗa ɗan Buran ɗin Gwandu babba

Daga Haruna Abdulrashid

Shugaban majalisar sarakuna ta jihar Kebbi, Mai martaba Sarkin Gwandu, Manjo-Janar Muhammadu Ilyasu Bashar Mni, ya karrama Shugaban hukumar jin daɗi da walwalar Alhazzai ta ƙasa, Malam Jalal Muhammad Arabi da sarautar (ƊAN BURAN GWANDU BABBA) inda mai martaba sarki ya aike da tawaga zuwa birnin tarayya Abuja domin gabatar da wannan karramawa zuwa ga Malam Jalal Arabi.

Da ya ke jawabi a madadin mai martaba sarkin Gwandu Alhaji Aminu Ahmad, Sarkin Fadan Gwandu ya bayyana cewa mai martaba sarkin Gwandu ya amince da bayar da wannan karramawa ga Malam Jalal ne a bisa jajircewa da kuma taimako da yake yiwa Alhazzan Najeriya tare da haɗin kai da yake bawa shugabanni a kan abin da ya shafi harkar aikin Hajji mussaman a bana.

Shi ma shugaban hukumar jin daɗin da walwalar Alhazai ta jihar Kebbi, Alhaji Faruƙu Musa Yaro Enabo, Jagaban Gwandu, ya bayyana jin daɗin shi matuƙa a kan wannan karramawar da aka yi wa maigidan shi.

Ya kuma yabawa mai martaba Sarkin Gwandu Manjo-Janar Muhammadu Ilyasu Bashar akan yadda yake gabatar da kyakkyawan jagoranci zuwa ga Al’ummar Gwandu.

Wannan bayar da takardar karramawa ta sarautar (ƊAN BURAN GWANDU) Sun haɗa da Alh Aminu Ahmed Sarkin Fadan Gwandu, Alh Aminu Abubakar Gulumbe Uban ƙasar Gulumbe, Alh. Mustapha Ka’oje Sarkin Bargun Ka’oje, Alh Lamiru Shehu Sakataren Sarakunan jihar Kebbi, Alh Faruƙu Musa Yaro Enabo Jagaban Gwandu, Alh Usman Osho da Alh Rilwanu Awwal.

Mai girma Shugaban hukumar Jin daɗi da walwalar Alhazzai ta jihar Kebbi, Malam Jalal Arabi, ya bayyana jin daɗin shi sosai ganin wanan karramawa da ya samu daga masarautar Gwandu.

Ya kuma ce jihar Kebbi ta zama gida a gareshi ganin yadda yake samun karramawa da mutuntawa a jihar ya kuma bayyana mana irin mutunci da zumunci dake tsakanin shi da shugaban hukumar Jin daɗi da walwalar Alhazzai ta jihar Kebbi.

Alh Faruku Musa Yaro Enabo Jagaban Gwandu ya kuma yi godiya da jinjina zuwa ga Maigirma Gwamnan jihar Kebbi His Excellency Comrd Dr. Nasir Idris Ƙauran Gwandu akan irin yadda yayi ɗawainiya ga Alhazzan jihar shi.

Continue Reading

Labarai

Mun gana da shugaba Tinubu mun isar masa saƙon al’umma – Shaikh Bala Lau

Published

on

Mun gana da shugaba Tinubu mun isar masa saƙon al'umma - Shaikh Bala Lau

Mun gana da shugaba Tinubu mun isar masa saƙon al’umma – Shaikh Bala Lau

Daga Idris Umar, Zariya

A ranar Alhamis tawagar malaman Najeriya ta gana da shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu dangane da halin da ƙasa ta ke ciki kan batun zanga-zanga da wasu ke ƙiran a yi dalilin halin matsi da tsadar rayuwa.

Rahoton sun nuna cewa jim kaɗanne bayan kammala ganawar, shugaban ƙungiyar Izala na ƙasa, Shaikh Abdullahi Bala Lau ya shaidawa manema labarai cewa shugaban ƙasa ya karɓi koken da suka je masa da shi.

“Mun faɗa mar halin da al’umma suke ciki na tsadar rayuwa, taɓarɓarewar tsaro da wahalar rayuwa, ya kuma ce dan Allah a ja hankalin al’umma a ba su haƙuri nan gaba kaɗan za a ga sauyi da gyara kan ƙorafe-ƙorafen da ake yi”. In ji Bala Lau.

KU KUMA KARANTA: Zanga-zanga ba gudu ba ja da baya – ‘Yan Najeriya

Daga nan kuma, Shaikh ɗin ya ja hankalin al’umma da su yi haƙuri su cigaba da addu’a, “ba mu da ƙasar da ta fi Najeriya kar mu rusa ƙasarmu da kanmu”. Inji Shaikh Bala Lau.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like