Aikin Hadin Gwiwa Tsakanin Jami’an Tsaro Zai Kawo Ci Gaba – Datti Ibrahim

0
319

Daga; MUSTAPHA IMRANA ABDULLAHI.

SHUGABAN rundunar mafarautan tsaron sa kai na Jihar Kaduna Kwamanda Datti Inrahim, ya bayyana wa manema labarai cewa samar da tsarin gudanar da ayyukan tsaro na hadin Gwiwa a tsakanin rundunonin tsaro zai taimaka a samu cimma bukatar da kowa ke fatan samu a bangaren tsaro.

Datti Ibrahim ya bayyana hakan ne lokacin da yake ke jawabi ga manema labarai jim kadan bayan halartar wani taro a tsakanin jami’an tsaro a Kaduna.

Datti Ibrahim ya ci gaba da cewa kamar su daman da suka san yadda Daji yake idan aka Sanya su a gaba za a cimma nasara kwarai, da za ta haifar da samun da mai idanu don haka ya na fatan za a dauki shawarar da yake bayarwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here