Connect with us

Labari

A Shirye Mu Ke Don Karbar Tubabbun Yan Boko Haram Da Za A Kawo Su Cikin Mu – Hardon Malkohi

Published

on

Daga, Sani Gazas Chinade, Damaturu.

A KOKARIN da su ke yi don amincewa da tubabbun yan Boko Haram da suka mika wuya wajen watsi da mummunar akidar nan ta ta’addanci, al’ummar garin Malkohi da ke karamar hukumar Yola ta kudu a Jihar Adamawa sun bayyana cewar, a shirye suke don karbar tubabbun ‘ya’yan Kungiyar ta Boko Haram da suka mika wuya don son komawa cikin al’umma.

Bayanin tabbatar da wannan abu dai ya fito ne daga bakin Hardon garin na Malkohi wadda sakataren sa Alhaji Bashir Aliyu ya wakilta yayin da jami’an hukumar nan ta kula da hakkin Dan Adam (NHRC) karkashin babban jami’inta Hillary Ogbonna da kuma jami’ar kula da harkokin yada labarai a hukumar Hajiya Fatima Agwai Mohammed tare da tawagar manema labaran da suke karbar horo kan gudummawar da za su iya bayarwa dangane da wayar da kan al’umma kan yafiya da Adalci ga al’ummar da ke da alaka da matsalar Boko Haram suka ziyarci garin na Malkohi don ganewa idon su irin halin da ‘yan Gudin Hijirar da ke Sansanin Malkohin ke ciki.

Hardon na Malkohi ya ci gaba da cewar, su mazauna wannan gari a Kullum a shirye su ke don ganin sun amince da karbar duk wasu tubabbun’ yan kungiyar ta Boko Haram da za a kawo gare su don zaunawa da su matukar hukumomin da abin ya shafa sun tantance su.

Ya kara da cewar a halin da ake ciki  shekaru uku da suka gabata an kawo musu wasu tubabbun na Boko Haram su kimanin 6 hade da iyalen su da aka tantance daga Gombe wadanda a yanzu suke tare da su.

Da jami’ar hukumar ta NHRC Fatima Agwai ke tambayar sa a kan ko daga lokacin da suka karbi wadannan tubabbun ko akwai wata matsala da suka fuskanta tare da su? Sai ya amsa da cewar lalle har kawowa ya yau ba mu taba fuskanta matsala ba tare da su, muna zaune lafiya da su, don har gonakin noma da wuraren sana’a muka ba su kuma ya zama wajibi da mu zama masu yafiya domin ta hanyar yafiya zamu samu zaman lafiya mai inganci. 

Tun farko da ta ke bayyana manufar zuwan su. babbar jami’ar yada labarai ta Hukumar ta NHRC Fatima Agwai ta bayyana wa Hardon na Malkohi cewar, sun kawo ziyarar ne don saduwa da su da kuma ‘yan Gudin hijirar da ke tare da su don jin irin damuwar su kana su kuma neme su da su zama masu yafiya da Adalci a tsakanin juna.

Shi ma da ya ke jawabi shugaban Sansanin ‘ yan Gudin Hijira na garin Malkohi Malam Umar Abubakar cewa, ya yi sun dade cikin wannan sansani kuma sun zo ne daga garin Gwoza akysarin su  sakamakon matsalar Boko Haram da suka tarwatsa su. 

Ya kara da cewa a yanzu haka sun dade a wannan sansani na Malkohi wanda a baya suna da ‘yan Hijira sama da dubu biyar amma sannu a hankali sama da dubu 3500 sun koma yankin su na Gwoza sakamakon zaman lafiya da ya fara wanzuwa. 

Ya kuma ce suna da koke ga gwamnati cewar da ta taimaka musu da abubuwan more rayuwa musamman abinci da sauran su kasancewar a halin yanzu suna fama da karancin abincin. 

Wakilin mu ya samu ganawa da daya daga cikin tubabbun Boko Haram din da ke sansanin na Malkohi mai suna Adamu Usman da aka ki amincewa da daukar hotonsa saboda matakan tsaro, ya bayyana cewar, shi yanzu sai godiya ga Allah SWT da ya kaddara ya tuba ya dawo cikin jama’ar sa, kuma yana godewa jama’ar sa da suka karbe shi tare da yafe masa abubuwan da suka faru a baya. 

Malam Adamu Usman ya kuma yi kira ga sauran ‘yan Uwansa da har yanzu suna cikin kungiyar ta Boko Haram da su watsar da wannan muguwar akida su dawo su mika wuya tare da watsar da malaman su kar su ji tsoron komai su taho za a karbe su ba za a musu komai ba. 

Daga nan sai hukumar ta NHRC ta mika kayayyakin tallafin da ta kaiwa ‘yan gudun Hijirar (IDPs) da suka hada da kwalayen Indomie da taliya da Makamantan su. 

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labari

EMAS69 • LINK ALTERNATIF SPORTBOOK SBOBET

Published

on

By

Emas69 adalah bandar taruhan sportbook sbobet terlengkap yang saat ini sangat dikenal seluruh masyarakat Indonesia dengan melalui link alternatif Emas69. Pada permainan taruhan sportbook, setiap pertandingan sepak bola yang dilangsungkan dapat dijadikan sebagai tempat bagi seluruh masyarakat Indonesia untuk melakukan taruhan dengan menggunakan uang asli. permainan taruhan bola online dapat dilakukan dengan bebas sesuai dengan pertandingan yang berlangsung dan juga team sepak bola yang disenangi untuk memperoleh kemenangan dan kepuasan dari setiap taruhan sportbook di situs Emas69.

Continue Reading

Labari

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Published

on

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi - TUC/NLC

Albashi mafi ƙaranci: Da babu gara ba daɗi – TUC/NLC

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

Gamayyar ƙungiyar ƙwadagon Najeriya ta ce tayin Naira 70,000 da shugaba Tinubu ya yi a matsayin mafi ƙarancin albashi da babu ne gara ba daɗi.

Shugabannin ƙwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun ƙwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.

KU KUMA KARANTA:NLC ta ƙira taron gaggawa bayan gwamnati ta jingine batun ƙarin albashi

Wannan dai na nuna a karo na farko tun neman mafi ƙarancin albashi mafi yawa a Najeriya Naira 615,00 ya sauƙo Naira 477,000, shugabannin ƙwadagon sun maida wuƙa kube ta hanyar yin na’am da tayin da gwamnati ta yi.

Bayan kammala ganawa babban sakataren ƙungiyar ƙwadagon ta TUC Komared Nuhu Toro ya ce sun amshi tayin da gabatar da hakan gaban majalisun su “mun kai majalisar ƙolinmu, tayin da shugaban ƙasa ya bayar sun kuma lamunta da shi da fatan Allah ya sa albarka…ai Naira 70,000 ɗin nan da babu ne gara ba daɗi.

Tuni ma’aikata na sassa daban-daban suka fara maida martani da mafi sauƙin shi ne na nuna ba abun da suka iya don jagorori sun miƙa wuya.

Malamin makaranta Muhammad Bello Nawaila ya ce ba wani tasiri da mafi ƙarancin albashin zai yi in an duba ɗan karen tsadar rayuwa.

Ita ma ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin arewa CNG da ke marawa gwagwarmayar ma’aikatan baya ta ce matuƙar shugaba Tinubu bai yi garambawul ga lamuran walwalar ma’aikata da matasa ba, za a iya fuskantar ƙalubale “mu na gujewa guguwar juyin juya hali a Najeriya matuƙar gwamnati ba ta farka ta ɗauki matakan gaskiya na zahiri ba.”

Alamu na nuna batun neman ƙarin mafi ƙarancin albashi zai dakata zuwa wani lokaci don ‘yan ƙwadagon sun yaɗa gora sai komawa kan batun tsadar rayuwa.

Continue Reading

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like