‘Yan sanda a Ogun, sun kama wani ɗauke da gawar mutum

Rundunar ‘yan sandan jihar Ogun ta ce an kama wani Babatunde Kolawole da ake zargin an same shi da sabon gawar mutum, tare da miƙa shi ga jami’anta a yankin Ado/Odo-Ota da ke jihar.

SP Omolola Odutola, jami’in hulɗa da jama’a na ‘yan sanda (PPRO), wanda ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi a Ota, Ogun, ya ce ‘yan sandan Amotekun ne suka kama wanda ake zargin.

A cewarta, jami’in ‘yan sanda na DPO, Sango-Ota, CSP Saleh Ɗahiru, ya samu rahoton Amotekun inda ya kai wanda ake zargi, Kolawole, a gidan yari.

“An fara bincike na farko kan lamarin. “Ko da yake wanda ake zargin bai musanta faruwar lamarin ba, amma ya yi iƙirarin cewa shi likita ne wanda ke yunƙurin tada marigayin.

“Duk da haka, har yanzu ba a san yadda wanda ake zargin ya samu gawar a cikin daren ba,” in ji ta.

KU KUMA KARANTA: EFCC ta kama mutane 23 da ake zargi da damfara ta yanar gizo

PPRO ya ce kawo yanzu, babu wanda ya fito ya ɗauki gawar, kuma wanda ake zargin bai bayyana wani bayani game da asalin gawar ba, don baiwa ‘yan sanda damar tattara ƙarin bayanai da kuma warware lamarin.

Ta ƙara da cewa an kai gawar zuwa babban asibitin Ifo domin gudanar da bincike.

Odutola ya buƙaci al’umma da su baiwa ‘yan sanda duk wani bayani mai amfani da ya shafi lamarin.

Ta kuma ce al’ummar yankin za su iya taimakawa ‘yan sanda wajen gudanar da bincike ta hanyar yin ƙarin haske kan lamarin.


Comments

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *